السورة: Suratul Baqara

الآية : 105

مَّا يَوَدُّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَلَا ٱلۡمُشۡرِكِينَ أَن يُنَزَّلَ عَلَيۡكُم مِّنۡ خَيۡرٖ مِّن رَّبِّكُمۡۚ وَٱللَّهُ يَخۡتَصُّ بِرَحۡمَتِهِۦ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ

Waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushrikai ba sa qaunar a saukar muku da wani alheri daga Ubangijinku, sai dai Allah kuwa Yana kevance wanda Ya ga dama da rahamarsa, Allah kuma Mai babbar falala ne



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 28

لَّا يَتَّخِذِ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَوۡلِيَآءَ مِن دُونِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۖ وَمَن يَفۡعَلۡ ذَٰلِكَ فَلَيۡسَ مِنَ ٱللَّهِ فِي شَيۡءٍ إِلَّآ أَن تَتَّقُواْ مِنۡهُمۡ تُقَىٰةٗۗ وَيُحَذِّرُكُمُ ٱللَّهُ نَفۡسَهُۥۗ وَإِلَى ٱللَّهِ ٱلۡمَصِيرُ

Kada muminai su riqi kafirai a matsayin masoya su qyale muminai; duk wanda kuwa ya aikata haka, to shi ba komai ne ba a wurin Allah, sai dai in don ku kare kanku ne daga gare su. Kuma Allah Yana tsoratar da ku kansa. Kuma zuwa ga Allah makoma take



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 98

قُلۡ يَـٰٓأَهۡلَ ٱلۡكِتَٰبِ لِمَ تَكۡفُرُونَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ وَٱللَّهُ شَهِيدٌ عَلَىٰ مَا تَعۡمَلُونَ

Ka ce: “Ya ku Ma’abota Littafi, don me kuke kafirce wa ayoyin Allah, kuma alhalin Allah Mai ba da shaida ne ga abin da kuke aikatawa?”



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 99

قُلۡ يَـٰٓأَهۡلَ ٱلۡكِتَٰبِ لِمَ تَصُدُّونَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ مَنۡ ءَامَنَ تَبۡغُونَهَا عِوَجٗا وَأَنتُمۡ شُهَدَآءُۗ وَمَا ٱللَّهُ بِغَٰفِلٍ عَمَّا تَعۡمَلُونَ

Ka ce: “Ya ku Ma’abota Littafi, don me kuke kange wanda ya yi imani daga hanyar Allah, kuna son ta zamo karkatacciya, kuma alhali ku da kanku masu shaida ne, kuma Allah ba gafalalle ne game da abin da kuke aikatawa ba?”



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 100

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِن تُطِيعُواْ فَرِيقٗا مِّنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ يَرُدُّوكُم بَعۡدَ إِيمَٰنِكُمۡ كَٰفِرِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka bi wani vangare na waxanda aka ba wa Littafi, to za su mayar da ku kafirai bayan imaninku



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 101

وَإِذَا ضَرَبۡتُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَلَيۡسَ عَلَيۡكُمۡ جُنَاحٌ أَن تَقۡصُرُواْ مِنَ ٱلصَّلَوٰةِ إِنۡ خِفۡتُمۡ أَن يَفۡتِنَكُمُ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْۚ إِنَّ ٱلۡكَٰفِرِينَ كَانُواْ لَكُمۡ عَدُوّٗا مُّبِينٗا

Kuma idan kun yi tafiya a bayan qasa, to babu laifi a kanku ku yi sallar qasaru[1], in kun ji tsoron kafirai su fitine ku[2]. Lalle kafirai sun kasance maqiya ne, masu bayyana qiyayya a gare ku


1- Watau ku taqaita salloli masu raka’a huxu zuwa raka’a biyu.


2- Ko da yake an ambaci halin tsoron fitinar kafirai, to amma wannan ba sharaxi ba ne, duk wanda yake a halin tafiya yana iya yin sallar qasaru.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 139

ٱلَّذِينَ يَتَّخِذُونَ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَوۡلِيَآءَ مِن دُونِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۚ أَيَبۡتَغُونَ عِندَهُمُ ٱلۡعِزَّةَ فَإِنَّ ٱلۡعِزَّةَ لِلَّهِ جَمِيعٗا

Su ne waxanda suke riqar kafirai a matsayin masoya, su qyale muminai. Shin suna neman wata xaukaka ce a wurinsu? To lalle xaukaka gaba xaya ta Allah ce[1]


1- Watau shi ne yake bayar da girma, kuma ga muminai kaxai yake ba da shi, don haka munafukai ba za su same shi ba.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 140

وَقَدۡ نَزَّلَ عَلَيۡكُمۡ فِي ٱلۡكِتَٰبِ أَنۡ إِذَا سَمِعۡتُمۡ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ يُكۡفَرُ بِهَا وَيُسۡتَهۡزَأُ بِهَا فَلَا تَقۡعُدُواْ مَعَهُمۡ حَتَّىٰ يَخُوضُواْ فِي حَدِيثٍ غَيۡرِهِۦٓ إِنَّكُمۡ إِذٗا مِّثۡلُهُمۡۗ إِنَّ ٱللَّهَ جَامِعُ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ وَٱلۡكَٰفِرِينَ فِي جَهَنَّمَ جَمِيعًا

Kuma haqiqa Ya saukar muku a cikin littafi[1] cewa, idan kuka ji ayoyin Allah ana kafirce musu, ana izgili da su, to kar ku zauna tare da su har sai sun shiga cikin wani zancen daban ba wannan ba. Lalle in har kuka zauna tare da su, to kun zama kamarsu. Lalle Allah Mai tattara munafuqai ne da kafirai cikin wutar Jahannama gaba xaya


1- Watau a cikin Alqur’ani a Suratul An’am, aya ta 68 inda Allah ya haramta wa muminai zama a inda ake yi wa shari’ar Allah izgili da rashin kunya.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 144

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَّخِذُواْ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَوۡلِيَآءَ مِن دُونِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۚ أَتُرِيدُونَ أَن تَجۡعَلُواْ لِلَّهِ عَلَيۡكُمۡ سُلۡطَٰنٗا مُّبِينًا

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku riqi kafirai a matsayin masoya ku bar muminai. Shin kuna so ku ba wa Allah wata hujja mabayyaniya ne a kanku?



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 57

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَّخِذُواْ ٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ دِينَكُمۡ هُزُوٗا وَلَعِبٗا مِّنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ مِن قَبۡلِكُمۡ وَٱلۡكُفَّارَ أَوۡلِيَآءَۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku riqi waxanda suke yin izgili da wasa da addininku, waxanda aka bai wa Littafi tun kafinku, da kuma kafirai, a matsayin masoya, kuma ku kiyaye dokokin Allah, in har da gaske ku muminai ne



السورة: Suratul An’am

الآية : 68

وَإِذَا رَأَيۡتَ ٱلَّذِينَ يَخُوضُونَ فِيٓ ءَايَٰتِنَا فَأَعۡرِضۡ عَنۡهُمۡ حَتَّىٰ يَخُوضُواْ فِي حَدِيثٍ غَيۡرِهِۦۚ وَإِمَّا يُنسِيَنَّكَ ٱلشَّيۡطَٰنُ فَلَا تَقۡعُدۡ بَعۡدَ ٱلذِّكۡرَىٰ مَعَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma idan ka ga waxanda suke kutsawa cikin ayoyinmu (suna izgili), to ka rabu da su, har sai sun canja wani zancen da ba wancan ba. Amma in da Shaixan zai mantar da kai kuwa, to bayan ka tuna kar ka sake zama tare da azzalumai



السورة: Suratut Tauba

الآية : 23

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَّخِذُوٓاْ ءَابَآءَكُمۡ وَإِخۡوَٰنَكُمۡ أَوۡلِيَآءَ إِنِ ٱسۡتَحَبُّواْ ٱلۡكُفۡرَ عَلَى ٱلۡإِيمَٰنِۚ وَمَن يَتَوَلَّهُم مِّنكُمۡ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku xauki iyayenku da ‘yan’uwanku masoya muddin dai sun fifita kafirci a kan imani. Duk kuwa waxanda suka xauke su (masoya) daga cikinku to waxannan su ne azzalumai



السورة: Suratu Hud

الآية : 113

وَلَا تَرۡكَنُوٓاْ إِلَى ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ فَتَمَسَّكُمُ ٱلنَّارُ وَمَا لَكُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ مِنۡ أَوۡلِيَآءَ ثُمَّ لَا تُنصَرُونَ

Kuma kada ku karkata zuwa ga waxanda suka yi zalunci, sai wuta ta shafe ku, ba ku kuwa da wasu majivinta lamura ba Allah ba, sannan ba za a taimake ku ba



السورة: Suratul Mumtahana

الآية : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَّخِذُواْ عَدُوِّي وَعَدُوَّكُمۡ أَوۡلِيَآءَ تُلۡقُونَ إِلَيۡهِم بِٱلۡمَوَدَّةِ وَقَدۡ كَفَرُواْ بِمَا جَآءَكُم مِّنَ ٱلۡحَقِّ يُخۡرِجُونَ ٱلرَّسُولَ وَإِيَّاكُمۡ أَن تُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ رَبِّكُمۡ إِن كُنتُمۡ خَرَجۡتُمۡ جِهَٰدٗا فِي سَبِيلِي وَٱبۡتِغَآءَ مَرۡضَاتِيۚ تُسِرُّونَ إِلَيۡهِم بِٱلۡمَوَدَّةِ وَأَنَا۠ أَعۡلَمُ بِمَآ أَخۡفَيۡتُمۡ وَمَآ أَعۡلَنتُمۡۚ وَمَن يَفۡعَلۡهُ مِنكُمۡ فَقَدۡ ضَلَّ سَوَآءَ ٱلسَّبِيلِ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku riqi maqiyana kuma maqiyanku masoya, kuna nuna musu soyayya, alhali kuwa sun kafirce wa abin da ya zo muku na gaskiya, suna fitar da Manzo har da ku kanku don kun yi imani da Allah Ubangijinku, idan har kun zamanto kun fito don yin jihadi saboda Ni da kuma neman yardata. Kuna voye qaunarku gare su, alhali kuwa Ina sane da abin da kuka voye da kuma abin da kuka bayyana. Duk kuwa wanda ya aikata haka daga cikinku, to haqiqa ya vace wa hanya madaidaiciya



السورة: Suratul Mumtahana

الآية : 2

إِن يَثۡقَفُوكُمۡ يَكُونُواْ لَكُمۡ أَعۡدَآءٗ وَيَبۡسُطُوٓاْ إِلَيۡكُمۡ أَيۡدِيَهُمۡ وَأَلۡسِنَتَهُم بِٱلسُّوٓءِ وَوَدُّواْ لَوۡ تَكۡفُرُونَ

Idan suka samu nasara a kanku za su zama abokan gabanku, kuma za su miqa hannayensu da harsunansu zuwa gare ku don munanawa, sun kuma yi burin ina ma da za ku kafirta



السورة: Suratul Mumtahana

الآية : 8

لَّا يَنۡهَىٰكُمُ ٱللَّهُ عَنِ ٱلَّذِينَ لَمۡ يُقَٰتِلُوكُمۡ فِي ٱلدِّينِ وَلَمۡ يُخۡرِجُوكُم مِّن دِيَٰرِكُمۡ أَن تَبَرُّوهُمۡ وَتُقۡسِطُوٓاْ إِلَيۡهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُقۡسِطِينَ

Allah bai hana ku ba game da waxanda ba su yaqe ku don addini ba, ba su kuma fitar da ku daga gidajenku ba, kan ku kyautata musu, ku kuma yi musu adalci. Lalle Allah Yana son masu adalci



السورة: Suratul Mumtahana

الآية : 9

إِنَّمَا يَنۡهَىٰكُمُ ٱللَّهُ عَنِ ٱلَّذِينَ قَٰتَلُوكُمۡ فِي ٱلدِّينِ وَأَخۡرَجُوكُم مِّن دِيَٰرِكُمۡ وَظَٰهَرُواْ عَلَىٰٓ إِخۡرَاجِكُمۡ أَن تَوَلَّوۡهُمۡۚ وَمَن يَتَوَلَّهُمۡ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Allah kawai Yana hana ku ne a kan ku qaunaci waxanda suka yaqe ku don addini, suka kuma fitar da ku daga gidajenku, suka kuma taimaka a kan fitar da ku. Duk kuwa wanda ya qaunace su, to waxannan su ne azzalumai



السورة: Suratul Mumtahana

الآية : 10

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِذَا جَآءَكُمُ ٱلۡمُؤۡمِنَٰتُ مُهَٰجِرَٰتٖ فَٱمۡتَحِنُوهُنَّۖ ٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِإِيمَٰنِهِنَّۖ فَإِنۡ عَلِمۡتُمُوهُنَّ مُؤۡمِنَٰتٖ فَلَا تَرۡجِعُوهُنَّ إِلَى ٱلۡكُفَّارِۖ لَا هُنَّ حِلّٞ لَّهُمۡ وَلَا هُمۡ يَحِلُّونَ لَهُنَّۖ وَءَاتُوهُم مَّآ أَنفَقُواْۚ وَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ أَن تَنكِحُوهُنَّ إِذَآ ءَاتَيۡتُمُوهُنَّ أُجُورَهُنَّۚ وَلَا تُمۡسِكُواْ بِعِصَمِ ٱلۡكَوَافِرِ وَسۡـَٔلُواْ مَآ أَنفَقۡتُمۡ وَلۡيَسۡـَٔلُواْ مَآ أَنفَقُواْۚ ذَٰلِكُمۡ حُكۡمُ ٱللَّهِ يَحۡكُمُ بَيۡنَكُمۡۖ وَٱللَّهُ عَلِيمٌ حَكِيمٞ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan muminai mata sun zo muku suna masu yin hijira, sai ku jarraba su; Allah ne Ya fi sanin imaninsu; to idan kuka san cewa su muminai ne, to kada ku mayar da su wurin kafirai; su ba halal ba ne gare su (kafirai), su ma (kafiran) ba halal ba ne a gare su; kuma ku ba su abin da suka kashe. Kuma babu laifi a kanku ku aure su idan kun ba su sadakinsu. Kada kuma ku riqe igiyar auren mata kafirai, ku tambayi abin da kuka kashe, su ma su tambayi abin da suka kashe[1]. Wannan shi ne hukuncin Allah da Yake hukuntawa a tsakaninku. Allah kuma Masani ne, Mai hikima


1- Watau duk matan da suka yi ridda suka gudu zuwa wajen kafirai, to Musulmi su nemi kafiran su biya su abin da suka kashe wajen auren su. Su ma kafiran su nemi Musulmi su biya su sadakin matansu da suka musulunta suka gudo wajen Musulmi.


السورة: Suratul Mumtahana

الآية : 11

وَإِن فَاتَكُمۡ شَيۡءٞ مِّنۡ أَزۡوَٰجِكُمۡ إِلَى ٱلۡكُفَّارِ فَعَاقَبۡتُمۡ فَـَٔاتُواْ ٱلَّذِينَ ذَهَبَتۡ أَزۡوَٰجُهُم مِّثۡلَ مَآ أَنفَقُواْۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ ٱلَّذِيٓ أَنتُم بِهِۦ مُؤۡمِنُونَ

Idan wasu matanku sun guje muku zuwa ga kafirai, sai kuka yi yaqi kuka samu galaba, to ku bai wa waxanda matansu suka guje musu kamar abin da suka kashe[1]. Ku kuma ku kiyaye dokokin Allah wanda kuke imani da Shi


1- Watau daga ganimar da aka samu ta yaqi.


السورة: Suratul Mumtahana

الآية : 12

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ إِذَا جَآءَكَ ٱلۡمُؤۡمِنَٰتُ يُبَايِعۡنَكَ عَلَىٰٓ أَن لَّا يُشۡرِكۡنَ بِٱللَّهِ شَيۡـٔٗا وَلَا يَسۡرِقۡنَ وَلَا يَزۡنِينَ وَلَا يَقۡتُلۡنَ أَوۡلَٰدَهُنَّ وَلَا يَأۡتِينَ بِبُهۡتَٰنٖ يَفۡتَرِينَهُۥ بَيۡنَ أَيۡدِيهِنَّ وَأَرۡجُلِهِنَّ وَلَا يَعۡصِينَكَ فِي مَعۡرُوفٖ فَبَايِعۡهُنَّ وَٱسۡتَغۡفِرۡ لَهُنَّ ٱللَّهَۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ya kai wannan Annabi, idan muminai mata suka zo maka suna yi maka mubaya’a a kan ba za su yi shirka da Allah ba, kuma ba za su yi sata ba, ba kuma za su yi zina ba, kuma ba za su kashe ‘ya’yansu ba, kuma ba za su zo da wani qage ba wanda za su qirqira (game da xan da suka haifa) a tsakanin hannayensu da qafafuwansu[1], kuma ba za su sava maka ba game da wani aiki na kirki, to sai ka yi musu mubaya’a, ka kuma nema musu gafarar Allah. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai


1- Kamar yadda suke yi a jahiliyya idan mace ta yi zina da mazaje da yawa sai ta zavi xaya ta danganta masa xan da ta haifa.


السورة: Suratul Mumtahana

الآية : 13

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَوَلَّوۡاْ قَوۡمًا غَضِبَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمۡ قَدۡ يَئِسُواْ مِنَ ٱلۡأٓخِرَةِ كَمَا يَئِسَ ٱلۡكُفَّارُ مِنۡ أَصۡحَٰبِ ٱلۡقُبُورِ

Ya ku waxanda kuka yi imani, kada ku jivinci mutanen da Allah ya yi fushi da su[1], haqiqa sun xebe qauna daga lahira kamar yadda kafirai suka xebe qauna daga na qabarurruka[2]


1- Su ne Yahudawan, waxanda saboda yawan savonsu da kafircinsu har Allah ya yi fushi da su.


2- Watau bayan an nuna musu makomarsu a wutar jahannama suka fitar da tsammanin samun kuvuta a ranar alqiyama.


السورة: Suratul Insan

الآية : 24

فَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ وَلَا تُطِعۡ مِنۡهُمۡ ءَاثِمًا أَوۡ كَفُورٗا

Saboda haka ka yi haquri da hukuncin Ubangijinka kada kuwa ka bi mai yawan savo ko mai yawan kafircewa daga cikinsu



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 1

قُلۡ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡكَٰفِرُونَ

Ka ce: “Ya ku waxannan kafirai



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 2

لَآ أَعۡبُدُ مَا تَعۡبُدُونَ

“Ba zan bauta wa abin da kuke bauta wa ba



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 3

وَلَآ أَنتُمۡ عَٰبِدُونَ مَآ أَعۡبُدُ

“Ku kuma ba masu bautar abin da nake bauta wa ba ne



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 4

وَلَآ أَنَا۠ عَابِدٞ مَّا عَبَدتُّمۡ

“Ni kuma ba mai bauta wa abin da kuka bauta wa ba ne



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 5

وَلَآ أَنتُمۡ عَٰبِدُونَ مَآ أَعۡبُدُ

“Ku ma ba za ku bauta wa abin da nake bauta wa ba



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 6

لَكُمۡ دِينُكُمۡ وَلِيَ دِينِ

“Addininku na gare ku, ni ma kuma addinina na gare ni[1].”


1- Annabi () ya ga wani yana karanta wannan Surar sai ya ce: “Amma dai wannan haqiqa ya kuvuta daga shirka”.