السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 41

فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle Aljanna ita ce makoma



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 42

يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا

Suna tambayar ka game da alqiyama, yaushe ne lokacinta?



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 43

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ

Me ya gama ka da ambaton lokacinta?



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 44

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ

Zuwa ga Ubangijinka ne iyakacin saninta yake[1]


1- Watau Allah ne kaxai ya san lokacin aukuwarta.


السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 45

إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا

Kai dai kawai mai gargaxin wanda yake tsoron ta ne



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 46

كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا

Kai ka ce su ranar da za su gan ta ba su zauna ba (a duniya) face wani yammaci ko kuma hantsinta



السورة: Suratu Abasa

الآية : 33

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ

Sannan idan mai sa kurunta ta zo (watau busa ta farko)



السورة: Suratu Abasa

الآية : 34

يَوۡمَ يَفِرُّ ٱلۡمَرۡءُ مِنۡ أَخِيهِ

A ranar da mutum yake guje wa xan’uwansa



السورة: Suratu Abasa

الآية : 35

وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ

Da uwarsa da ubansa



السورة: Suratu Abasa

الآية : 36

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ

Da matarsa da ‘ya’yansa



السورة: Suratu Abasa

الآية : 37

لِكُلِّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ يَوۡمَئِذٖ شَأۡنٞ يُغۡنِيهِ

Kowane mutum daga cikinsu a wannan ranar yana da lamarin da ya sha kansa



السورة: Suratu Abasa

الآية : 38

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ مُّسۡفِرَةٞ

Wasu fuskoki a wannan ranar masu haske ne



السورة: Suratu Abasa

الآية : 39

ضَاحِكَةٞ مُّسۡتَبۡشِرَةٞ

Masu dariya, masu farin ciki



السورة: Suratu Abasa

الآية : 40

وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ عَلَيۡهَا غَبَرَةٞ

Wasu fuskokin kuma a ranar akwai qura a kansu



السورة: Suratu Abasa

الآية : 41

تَرۡهَقُهَا قَتَرَةٌ

Baqin ciki zai lulluve su



السورة: Suratu Abasa

الآية : 42

أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَفَرَةُ ٱلۡفَجَرَةُ

Waxannan su ne kafirai mavarnata



السورة: Suratul Infixar

الآية : 17

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Kuma kai me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



السورة: Suratul Infixar

الآية : 18

ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Sannan me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



السورة: Suratul Infixar

الآية : 19

يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ

(Ita ce) ranar da wani rai ba ya mallakar wani amfani ga wani rai; al’amari kuwa (gaba xayansa) a wannan ranar yana ga Allah



السورة: Suratul Fajr

الآية : 21

كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا

Ba haka ne ba, idan aka girgiza qasa matuqar girgiza



السورة: Suratul Fajr

الآية : 22

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا

Ubangijinka kuma Ya zo[1] tare da mala’iku sahu-sahu


1- Watau don yin hukunci a tsakanin bayinsa.


السورة: Suratul Fajr

الآية : 23

وَجِاْيٓءَ يَوۡمَئِذِۭ بِجَهَنَّمَۚ يَوۡمَئِذٖ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكۡرَىٰ

Aka kuma zo da Jahannama a wannan ranar. To fa a wannan ranar ne mutum zai tuna (sakacinsa), ta yaya wannan tunawar za ta yi masa amfani?



السورة: Suratul Fajr

الآية : 24

يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي قَدَّمۡتُ لِحَيَاتِي

Zai ce: “Kaitona, ina ma da na gabatar (da ayyukan alheri) a rayuwata!”



السورة: Suratul Fajr

الآية : 25

فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٞ

To a wannan ranar ba wani xaya da zai yi azaba irin azabarsa (watau Allah)



السورة: Suratul Fajr

الآية : 26

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٞ

Ba kuma xaya da zai yi xauri irin xaurinsa



السورة: Suratul Fajr

الآية : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa



السورة: Suratul Fajr

الآية : 28

ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ

Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda



السورة: Suratul Fajr

الآية : 29

فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي

Don haka ka shiga cikin bayina



السورة: Suratul Fajr

الآية : 30

وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي

Ka kuma shiga Aljannata



السورة: Suratuz Zalzala

الآية : 1

إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا

Idan aka girgiza qasa matuqar girgiza ta