السورة: Suratul Baqara

الآية : 62

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱلَّذِينَ هَادُواْ وَٱلنَّصَٰرَىٰ وَٱلصَّـٰبِـِٔينَ مَنۡ ءَامَنَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا فَلَهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Lalle waxanda suka yi imani da Yahudawa da Nasara da Sabi’awa[1], duk wanda ya yi imani da Allah da ranar Lahira kuma ya yi aiki na qwarai, to suna da ladansu a wurin Ubangijinsu, kuma babu tsoro a tare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba


1- Waxanda suka yi imani, su ne al’ummar Annabi Muhammadu (). Yahudawa, ana nufin mabiya Annabi Musa () kafin a shafe addininsa, ko kafin su gurvata shi. Nasara, ana nufin mabiya Annabi Isa () kafin a shafe addininsa ko kafin su gurvata shi. Sabi’awa, wasu qungiyoyi ne, daga cikinsu akwai masu aqidar kaxaita Allah da haramta duk wata alfasha da zalunci, duk da kasancewarsu ba bisa wani addini suke ba, to amma ba sa aikata shirka.


السورة: Suratul Baqara

الآية : 111

وَقَالُواْ لَن يَدۡخُلَ ٱلۡجَنَّةَ إِلَّا مَن كَانَ هُودًا أَوۡ نَصَٰرَىٰۗ تِلۡكَ أَمَانِيُّهُمۡۗ قُلۡ هَاتُواْ بُرۡهَٰنَكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Kuma (Yahudawa da Nasara) suka ce: “Babu mai shiga Aljanna sai wanda ya kasance Bayahude ko Banasare”. Waxannan burace-buracensu ne. Ka ce: “Ku kawo hujjarku idan kun kasance masu gaskiya”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 112

بَلَىٰۚ مَنۡ أَسۡلَمَ وَجۡهَهُۥ لِلَّهِ وَهُوَ مُحۡسِنٞ فَلَهُۥٓ أَجۡرُهُۥ عِندَ رَبِّهِۦ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

E! Wanda ya miqa fuskarsa ga Allah alhali yana mai kyautata aikinsa, to yana da ladansa a wajen Ubangijinsa, kuma babu tsoro a tare da su kuma ba za su yi baqin ciki ba



السورة: Suratul Baqara

الآية : 113

وَقَالَتِ ٱلۡيَهُودُ لَيۡسَتِ ٱلنَّصَٰرَىٰ عَلَىٰ شَيۡءٖ وَقَالَتِ ٱلنَّصَٰرَىٰ لَيۡسَتِ ٱلۡيَهُودُ عَلَىٰ شَيۡءٖ وَهُمۡ يَتۡلُونَ ٱلۡكِتَٰبَۗ كَذَٰلِكَ قَالَ ٱلَّذِينَ لَا يَعۡلَمُونَ مِثۡلَ قَوۡلِهِمۡۚ فَٱللَّهُ يَحۡكُمُ بَيۡنَهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فِيمَا كَانُواْ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَ

Yahudawa suka ce: “Nasara ba a kan komai suke ba”, su ma Nasara suka ce: “Yahudawa ba a kan komai suke ba”, alhalin dukkansu suna karanta Littafi. Kamar haka ne waxanda ba su da ilimi suka yi irin maganarsu. Kuma Allah zai yi hukunci a tsakaninsu ranar Alqiyama a kan abin da suka kasance suna savani a cikinsa



السورة: Suratul Baqara

الآية : 120

وَلَن تَرۡضَىٰ عَنكَ ٱلۡيَهُودُ وَلَا ٱلنَّصَٰرَىٰ حَتَّىٰ تَتَّبِعَ مِلَّتَهُمۡۗ قُلۡ إِنَّ هُدَى ٱللَّهِ هُوَ ٱلۡهُدَىٰۗ وَلَئِنِ ٱتَّبَعۡتَ أَهۡوَآءَهُم بَعۡدَ ٱلَّذِي جَآءَكَ مِنَ ٱلۡعِلۡمِ مَا لَكَ مِنَ ٱللَّهِ مِن وَلِيّٖ وَلَا نَصِيرٍ

Yahudawa da Nasara ba za su tava yarda da kai ba har sai ka bi addininsu. Ka ce: “Shiriyar Allah lalle ita ce shiriya”. Idan har ka bi son zuciyarsu bayan abin da ya zo maka na gaskiya, to ba ka da wani majivinci ko mai taimakonka wajen Allah



السورة: Suratul Baqara

الآية : 135

وَقَالُواْ كُونُواْ هُودًا أَوۡ نَصَٰرَىٰ تَهۡتَدُواْۗ قُلۡ بَلۡ مِلَّةَ إِبۡرَٰهِـۧمَ حَنِيفٗاۖ وَمَا كَانَ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

Kuma suka ce: “Ku zama Yahudawa ko Nasara za ku shiriya”. Ka ce: “A’a! (Za mu bi) addinin Ibrahimu ne wanda yake miqe totar, kuma bai zamo daga cikin masu shirka ba.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 14

وَمِنَ ٱلَّذِينَ قَالُوٓاْ إِنَّا نَصَٰرَىٰٓ أَخَذۡنَا مِيثَٰقَهُمۡ فَنَسُواْ حَظّٗا مِّمَّا ذُكِّرُواْ بِهِۦ فَأَغۡرَيۡنَا بَيۡنَهُمُ ٱلۡعَدَاوَةَ وَٱلۡبَغۡضَآءَ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِۚ وَسَوۡفَ يُنَبِّئُهُمُ ٱللَّهُ بِمَا كَانُواْ يَصۡنَعُونَ

Kuma daga cikin waxanda suka ce: “Lalle mu Nasara ne,” su ma Mun riqi alqawarinsu, sai suka bar wani kaso na abin da aka yi musu wa’azi da shi, sai Muka iza wutar gaba da qiyayya a tsakaninsu har zuwa ranar tashin alqiyama. Kuma da sannu Allah zai ba su labarin abin da suka kasance suna aikatawa



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 17

لَّقَدۡ كَفَرَ ٱلَّذِينَ قَالُوٓاْ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡمَسِيحُ ٱبۡنُ مَرۡيَمَۚ قُلۡ فَمَن يَمۡلِكُ مِنَ ٱللَّهِ شَيۡـًٔا إِنۡ أَرَادَ أَن يُهۡلِكَ ٱلۡمَسِيحَ ٱبۡنَ مَرۡيَمَ وَأُمَّهُۥ وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗاۗ وَلِلَّهِ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَاۚ يَخۡلُقُ مَا يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Lalle haqiqa, waxannan da suka ce: “Lalle Allah Shi ne Almasihu xan Maryamu” sun kafirta. Ka ce: “To wane ne ya isa ya hana Allah, idan Ya yi nufin Ya hallaka Almasihu xan Maryamu da mahaifiyarsa da duk wanda yake ban qasa gaba xaya? Allah kuwa Shi Yake mallakar abin da yake cikin sammai da qasa da kuma abin da yake tsakaninsu. Yana halittar abin da Ya ga dama. Kuma Allah Mai cikakken iko ne a kan komai.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 18

وَقَالَتِ ٱلۡيَهُودُ وَٱلنَّصَٰرَىٰ نَحۡنُ أَبۡنَـٰٓؤُاْ ٱللَّهِ وَأَحِبَّـٰٓؤُهُۥۚ قُلۡ فَلِمَ يُعَذِّبُكُم بِذُنُوبِكُمۖ بَلۡ أَنتُم بَشَرٞ مِّمَّنۡ خَلَقَۚ يَغۡفِرُ لِمَن يَشَآءُ وَيُعَذِّبُ مَن يَشَآءُۚ وَلِلَّهِ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَاۖ وَإِلَيۡهِ ٱلۡمَصِيرُ

Kuma Yahudawa da Nasara suka ce: “Mu ‘ya’yan Allah ne, kuma masoyansa.” Ka ce: “To don me Yake muku azaba a sanadiyyar zunubanku? Ba haka ne ba, ku mutane ne daga cikin waxanda Ya halitta. Yana yin gafara ga wanda Ya ga dama, kuma Yana yin azaba ga wanda Ya ga dama. Kuma mulkin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu na Allah ne, kuma zuwa gare Shi ne makoma take.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 47

وَلۡيَحۡكُمۡ أَهۡلُ ٱلۡإِنجِيلِ بِمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ فِيهِۚ وَمَن لَّمۡ يَحۡكُم بِمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡفَٰسِقُونَ

Lalle kuma ma’abota Linjila su yi hukunci da abin da Allah Ya saukar a cikinsa. Duk wanda bai yi hukunci da abin da Allah Ya saukar ba kuwa, to waxannan su ne fasiqai



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 51

۞يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَتَّخِذُواْ ٱلۡيَهُودَ وَٱلنَّصَٰرَىٰٓ أَوۡلِيَآءَۘ بَعۡضُهُمۡ أَوۡلِيَآءُ بَعۡضٖۚ وَمَن يَتَوَلَّهُم مِّنكُمۡ فَإِنَّهُۥ مِنۡهُمۡۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku riqi Yahudawa da Nasara masoya. Sashinsu masoya sashi ne. Duk kuwa cikinku wanda ya jivinci lamarinsu, to lalle shi yana cikinsu. Lalle Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 69

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱلَّذِينَ هَادُواْ وَٱلصَّـٰبِـُٔونَ وَٱلنَّصَٰرَىٰ مَنۡ ءَامَنَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا فَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Lalle waxanda suka yi imani da waxanda suke Yahudawa da Sabi’awa da Nasara, duk wanda ya yi imani da Allah da ranar qarshe, kuma ya yi aiki nagari, to babu jin tsoro a tattare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 72

لَقَدۡ كَفَرَ ٱلَّذِينَ قَالُوٓاْ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡمَسِيحُ ٱبۡنُ مَرۡيَمَۖ وَقَالَ ٱلۡمَسِيحُ يَٰبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ رَبِّي وَرَبَّكُمۡۖ إِنَّهُۥ مَن يُشۡرِكۡ بِٱللَّهِ فَقَدۡ حَرَّمَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِ ٱلۡجَنَّةَ وَمَأۡوَىٰهُ ٱلنَّارُۖ وَمَا لِلظَّـٰلِمِينَ مِنۡ أَنصَارٖ

Lalle haqiqa waxanda suka ce: “Lalle Allah Shi ne Almasihu xan Maryamu” sun kafirta. Shi kuwa Almasihu cewa ya yi: “Ya ku Bani-Isra’ila, ku bauta wa Allah Ubangijina kuma Ubangijinku. Lalle yadda al’amarin yake, duk wanda ya yi shirka da Allah, to haqiqa Allah Ya haramta masa shiga Aljanna, kuma makomarsa ita ce wuta, kuma azzalumai ba su da wasu mataimaka.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 73

لَّقَدۡ كَفَرَ ٱلَّذِينَ قَالُوٓاْ إِنَّ ٱللَّهَ ثَالِثُ ثَلَٰثَةٖۘ وَمَا مِنۡ إِلَٰهٍ إِلَّآ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞۚ وَإِن لَّمۡ يَنتَهُواْ عَمَّا يَقُولُونَ لَيَمَسَّنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٌ

Lalle haqiqa waxannan da suka ce: “Lalle Allah Shi ne na cikon (alloli) uku,”[1] sun kafirta. Babu kuwa wani abin bautawa na gaskiya, sai abin bauta Xaya tal. Idan ba su bar abin da suke faxa xin nan ba, lalle azaba mai raxaxi za ta shafi waxanda suka kafirta daga cikinsu


1- Ana nufin aqidar Nasara da suke cewa, abu uku ne suka haxu suka zama Allah, watau Isa da mahaifiyarsa Maryamu da kuma Allah.


السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 82

۞لَتَجِدَنَّ أَشَدَّ ٱلنَّاسِ عَدَٰوَةٗ لِّلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱلۡيَهُودَ وَٱلَّذِينَ أَشۡرَكُواْۖ وَلَتَجِدَنَّ أَقۡرَبَهُم مَّوَدَّةٗ لِّلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱلَّذِينَ قَالُوٓاْ إِنَّا نَصَٰرَىٰۚ ذَٰلِكَ بِأَنَّ مِنۡهُمۡ قِسِّيسِينَ وَرُهۡبَانٗا وَأَنَّهُمۡ لَا يَسۡتَكۡبِرُونَ

Tabbas lalle za ka samu cewa, mutanen da suka fi tsananin gaba da waxanda suka yi imani, su ne Yahudawa da waxanda suke mushirikai. Kuma tabbas lalle za ka sami waxanda suka fi kusanci wajen nuna qauna ga waxanda suka yi imani, su ne waxanda suka ce: “Lalle mu Nasara ne.” Wannan kuwa saboda a cikinsu akwai malamai da masu yawan ibada, don kuma lalle su ba sa yin girman kai



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 83

وَإِذَا سَمِعُواْ مَآ أُنزِلَ إِلَى ٱلرَّسُولِ تَرَىٰٓ أَعۡيُنَهُمۡ تَفِيضُ مِنَ ٱلدَّمۡعِ مِمَّا عَرَفُواْ مِنَ ٱلۡحَقِّۖ يَقُولُونَ رَبَّنَآ ءَامَنَّا فَٱكۡتُبۡنَا مَعَ ٱلشَّـٰهِدِينَ

Kuma idan sun ji abin da aka saukar wa wannan Manzo, za ka ga idanunsu suna zubar da hawaye, saboda abin da suka gane na gaskiya; suna cewa: “Ya Ubangijinmu, mun yi imani, don haka Ka rubuta mu cikin masu shaidawa



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 84

وَمَا لَنَا لَا نُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَمَا جَآءَنَا مِنَ ٱلۡحَقِّ وَنَطۡمَعُ أَن يُدۡخِلَنَا رَبُّنَا مَعَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلصَّـٰلِحِينَ

“Kuma me muke da shi da ba za mu yi imani da Allah da abin da ya zo mana na gaskiya ba, muna kuwa sa rai Ubangijinmu Ya shigar da mu cikin salihan bayi?”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 85

فَأَثَٰبَهُمُ ٱللَّهُ بِمَا قَالُواْ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ وَذَٰلِكَ جَزَآءُ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Sai Allah Ya saka musu saboda abin da suka faxa, da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, suna masu dauwama a cikinsu, kuma wannan shi ne sakamakon masu kyautatawa



السورة: Suratut Tauba

الآية : 30

وَقَالَتِ ٱلۡيَهُودُ عُزَيۡرٌ ٱبۡنُ ٱللَّهِ وَقَالَتِ ٱلنَّصَٰرَى ٱلۡمَسِيحُ ٱبۡنُ ٱللَّهِۖ ذَٰلِكَ قَوۡلُهُم بِأَفۡوَٰهِهِمۡۖ يُضَٰهِـُٔونَ قَوۡلَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِن قَبۡلُۚ قَٰتَلَهُمُ ٱللَّهُۖ أَنَّىٰ يُؤۡفَكُونَ

Yahudawa sun ce: “Uzairu xan Allah ne.” Nasara kuma suka ce: “Almasihu xan Allah ne.” Wannan faxarsu ce kawai da bakunansu; suna kwaikwayon faxar kafiran da suka gabace su ne. Allah Ya tsine musu. Ta qaqa ake kautar da su daga gaskiya?



السورة: Suratut Tauba

الآية : 31

ٱتَّخَذُوٓاْ أَحۡبَارَهُمۡ وَرُهۡبَٰنَهُمۡ أَرۡبَابٗا مِّن دُونِ ٱللَّهِ وَٱلۡمَسِيحَ ٱبۡنَ مَرۡيَمَ وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُوٓاْ إِلَٰهٗا وَٰحِدٗاۖ لَّآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۚ سُبۡحَٰنَهُۥ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Sun xauki malamansu da masu ibadarsu da kuma Almasihu xan Maryamu iyayen giji maimakon Allah[1], alhali kuwa ba abin da aka umarce su sai su bauta wa Abin bauta Xaya, babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. Ya tsarkaka daga abin da suke tara Shi da shi


1- Watau suna yi wa malamansu da masu bauta a cikinsu makauniyar biyayya, suna haramta musu halal, su kuma halatta musu haram. Nasara sun xauki Annabi Isa () abin bauta ba Allah ba.


السورة: Suratul Hajji

الآية : 17

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱلَّذِينَ هَادُواْ وَٱلصَّـٰبِـِٔينَ وَٱلنَّصَٰرَىٰ وَٱلۡمَجُوسَ وَٱلَّذِينَ أَشۡرَكُوٓاْ إِنَّ ٱللَّهَ يَفۡصِلُ بَيۡنَهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

Lalle waxanda suka yi imani da waxanda suka zama Yahudawa da Sabi’awa da waxanda suka zama Majusawa da kuma waxanda suka yi shirka, lalle Allah zai yi hukunci a tsakaninsu ranar alqiyama. Lalle Allah Mai ganin kowane abu ne



السورة: Suratul Hadid

الآية : 27

ثُمَّ قَفَّيۡنَا عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِم بِرُسُلِنَا وَقَفَّيۡنَا بِعِيسَى ٱبۡنِ مَرۡيَمَ وَءَاتَيۡنَٰهُ ٱلۡإِنجِيلَۖ وَجَعَلۡنَا فِي قُلُوبِ ٱلَّذِينَ ٱتَّبَعُوهُ رَأۡفَةٗ وَرَحۡمَةٗۚ وَرَهۡبَانِيَّةً ٱبۡتَدَعُوهَا مَا كَتَبۡنَٰهَا عَلَيۡهِمۡ إِلَّا ٱبۡتِغَآءَ رِضۡوَٰنِ ٱللَّهِ فَمَا رَعَوۡهَا حَقَّ رِعَايَتِهَاۖ فَـَٔاتَيۡنَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مِنۡهُمۡ أَجۡرَهُمۡۖ وَكَثِيرٞ مِّنۡهُمۡ فَٰسِقُونَ

Sannan a bayansu Muka biyar da manzanninmu, Muka kuma biyar da Isa xan Maryamu Muka kuma ba shi Linjila, kuma Muka sanya jin qai da rahama a cikin zukatan waxanda suka bi shi. Rahbaniyanci[1] kuma su ne suka qago shi, ba Mu wajabta musu shi ba, sai dai (Mun wajabta musu) neman yardar Allah, amma ba su kiyaye shi ba kamar yadda ya kamata; sai Muka bai wa waxanda suka yi imani daga cikinsu ladansu; da yawa kuwa fasiqai ne


1- Bidi’ar Rahbaniyanci ita ce, qaurace wa aure da barin cin daxaxan abubuwa na halal da haramta wa kai wasu abubuwa da Allah ya halatta.