السورة: Suratul A’araf

الآية : 8

وَٱلۡوَزۡنُ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡحَقُّۚ فَمَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

Awo kuma a wannan ranar gaskiya ne. Don haka duk wanda ma’aunansa suka yi nauyi, to waxannan su ne masu rabauta



السورة: Suratul A’araf

الآية : 9

وَمَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ خَسِرُوٓاْ أَنفُسَهُم بِمَا كَانُواْ بِـَٔايَٰتِنَا يَظۡلِمُونَ

Wanda kuwa ma’aunansa suka yi sakayau, to waxannan su ne waxanda suka yi hasarar kawunansu, saboda abin da suka kasance suna yi na zalunci da ayoyinmu



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 102

فَمَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

To waxanda ma’aunansu suka yi nauyi waxannan su ne masu babban rabo



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 103

وَمَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ خَسِرُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ فِي جَهَنَّمَ خَٰلِدُونَ

Waxanda kuwa ma’aunansu suka yi sakayau waxannan su ne waxanda suka yi asarar kawunansu, suna masu dawwama a cikin (wutar) Jahannama



السورة: Suratul Qari’a

الآية : 6

فَأَمَّا مَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ

To amma wanda ma’aunan ayyukansa suka yi nauyi



السورة: Suratul Qari’a

الآية : 7

فَهُوَ فِي عِيشَةٖ رَّاضِيَةٖ

To shi kam yana cikin rayuwa mai gamsarwa



السورة: Suratul Qari’a

الآية : 8

وَأَمَّا مَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ

Amma kuma duk wanda ma’aunan ayyukansa suka yi shafal



السورة: Suratul Qari’a

الآية : 9

فَأُمُّهُۥ هَاوِيَةٞ

To shi makomarsa (wutar) Hawiya ce