وَبَيۡنَهُمَا حِجَابٞۚ وَعَلَى ٱلۡأَعۡرَافِ رِجَالٞ يَعۡرِفُونَ كُلَّۢا بِسِيمَىٰهُمۡۚ وَنَادَوۡاْ أَصۡحَٰبَ ٱلۡجَنَّةِ أَن سَلَٰمٌ عَلَيۡكُمۡۚ لَمۡ يَدۡخُلُوهَا وَهُمۡ يَطۡمَعُونَ
A tsakaninsu kuma akwai wani shamaki. Kuma a kan tozon La’arafi akwai waxansu mazaje suna gane kowane (xan Aljanna da xan wuta) da alamominsu[1]. Kuma sai su kira ‘yan Aljanna cewa: “Amincin Allah ya tabbata a gare ku.” (Lokacin) ba su shige ta ba, amma suna kwaxayin (shigar ta)
1- Waxannan mazaje su ne waxanda kyawawan ayyukansu suka yi daidai da munanansu.
۞وَإِذَا صُرِفَتۡ أَبۡصَٰرُهُمۡ تِلۡقَآءَ أَصۡحَٰبِ ٱلنَّارِ قَالُواْ رَبَّنَا لَا تَجۡعَلۡنَا مَعَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ
Idan kuma an juyar da idanuwansu vangaren ‘yan wuta sai su ce: “Ya Ubangijinmu, kada Ka sanya mu tare da mutane azzalumai.”
وَنَادَىٰٓ أَصۡحَٰبُ ٱلۡأَعۡرَافِ رِجَالٗا يَعۡرِفُونَهُم بِسِيمَىٰهُمۡ قَالُواْ مَآ أَغۡنَىٰ عَنكُمۡ جَمۡعُكُمۡ وَمَا كُنتُمۡ تَسۡتَكۡبِرُونَ
Sai ‘yan tozon La’arafi su kira waxansu mazaje da suke gane su da alamominsu[1], sai su ce: “Taronku bai wadatar da ku da komai ba, da girman kan da kuka kasance kuna yi
1- Su ne shugabannin mushirikai waxanda sun san su tun a duniya, kuma a nan ma lahira sun shaida su da alamominsu na ‘yan wuta.