السورة: Suratus Shura

الآية : 5

تَكَادُ ٱلسَّمَٰوَٰتُ يَتَفَطَّرۡنَ مِن فَوۡقِهِنَّۚ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ يُسَبِّحُونَ بِحَمۡدِ رَبِّهِمۡ وَيَسۡتَغۡفِرُونَ لِمَن فِي ٱلۡأَرۡضِۗ أَلَآ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

Sammai suna neman su tsattsage ta samansu (don girmansa). Mala’iku kuma suna yin tasbihi da yabon Ubangijinsu, suna kuma neman gafara ga waxanda suke cikin qasa. Ku saurara, Lalle Allah Shi ne Mai gafara, Mai rahama



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 77

وَنَادَوۡاْ يَٰمَٰلِكُ لِيَقۡضِ عَلَيۡنَا رَبُّكَۖ قَالَ إِنَّكُم مَّـٰكِثُونَ

Suka kuma yi kiran: “Ya (kai mai tsaron wuta) Maliku, Ubangijinka Ya kashe mu mana!” Ya ce: “Lalle ku masu dawwama ne.”



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 80

أَمۡ يَحۡسَبُونَ أَنَّا لَا نَسۡمَعُ سِرَّهُمۡ وَنَجۡوَىٰهُمۚ بَلَىٰ وَرُسُلُنَا لَدَيۡهِمۡ يَكۡتُبُونَ

Ko suna tsammanin cewa Mu ba Ma jin asirinsu da ganawarsu ne? Ba haka ba ne, manzanninmu suna tare da su suna rubutawa



السورة: Suratu Qaf 

الآية : 17

إِذۡ يَتَلَقَّى ٱلۡمُتَلَقِّيَانِ عَنِ ٱلۡيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ قَعِيدٞ

Yayin da (mala’iku biyu) masu haxuwa suka haxu ta dama da ta hagu suna zaune



السورة: Suratu Qaf 

الآية : 18

مَّا يَلۡفِظُ مِن قَوۡلٍ إِلَّا لَدَيۡهِ رَقِيبٌ عَتِيدٞ

Ba wata magana da zai furta face a tare da shi akwai (mala’ika) mai kula kuma halartacce



السورة: Suratu Qaf 

الآية : 21

وَجَآءَتۡ كُلُّ نَفۡسٖ مَّعَهَا سَآئِقٞ وَشَهِيدٞ

Kuma kowane rai ya zo a tare da shi akwai mai kora da mai shaida[1]


1- Watau mala’iku biyu tare da kowane mutum, xaya yana kora shi; xaya kuma mai ba da shaida game da shi.


السورة: Suratu Qaf 

الآية : 22

لَّقَدۡ كُنتَ فِي غَفۡلَةٖ مِّنۡ هَٰذَا فَكَشَفۡنَا عَنكَ غِطَآءَكَ فَبَصَرُكَ ٱلۡيَوۡمَ حَدِيدٞ

Haqiqa ka kasance a cikin gafala game da wannan, sai Muka yaye maka yanarka, to ganinka a yau tangaran yake



السورة: Suratu Qaf 

الآية : 23

وَقَالَ قَرِينُهُۥ هَٰذَا مَا لَدَيَّ عَتِيدٌ

Mala’ikan da yake tare da shi kuma ya ce: “Wannan shi ne abin da yake hallare a tare da ni.”



السورة: Suratun Najm

الآية : 26

۞وَكَم مِّن مَّلَكٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغۡنِي شَفَٰعَتُهُمۡ شَيۡـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ أَن يَأۡذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرۡضَىٰٓ

Mala’iku nawa ne a cikin sammai cetonsu ba ya amfanar da komai sai da izinin Allah ga waxanda Ya ga dama Ya kuma yarda (da shi)?



السورة: Suratun Najm

الآية : 27

إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ لَيُسَمُّونَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ تَسۡمِيَةَ ٱلۡأُنثَىٰ

Lalle waxanda ba sa yin imani da ranar lahira suna kiran mala’iku da sunan mata



السورة: Suratun Najm

الآية : 28

وَمَا لَهُم بِهِۦ مِنۡ عِلۡمٍۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّۖ وَإِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـٔٗا

Kuma ba su da wani ilimi game da haka; ba abin da suke bi sai zato; shi kuma zato, lalle ba ya wadatar da komai game da gaskiya



السورة: Suratut Tahrim

الآية : 6

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ قُوٓاْ أَنفُسَكُمۡ وَأَهۡلِيكُمۡ نَارٗا وَقُودُهَا ٱلنَّاسُ وَٱلۡحِجَارَةُ عَلَيۡهَا مَلَـٰٓئِكَةٌ غِلَاظٞ شِدَادٞ لَّا يَعۡصُونَ ٱللَّهَ مَآ أَمَرَهُمۡ وَيَفۡعَلُونَ مَا يُؤۡمَرُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku kare kawunanku da iyalanku daga wuta (wadda) makamashinta mutane ne da duwatsu, masu kula da ita mala’iku ne masu kaushin hali, masu tsananin gaske, ba sa sava wa Allah abin da Ya umarce su, suna kuma aikata abin da ake umartar su



السورة: Suratul Haqqa

الآية : 17

وَٱلۡمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرۡجَآئِهَاۚ وَيَحۡمِلُ عَرۡشَ رَبِّكَ فَوۡقَهُمۡ يَوۡمَئِذٖ ثَمَٰنِيَةٞ

Mala’iku kuma suna a sasanninta. A wannan ranar kuma (mala’iku) takwas za su xauki Al’arshin Ubangijinka a samansu



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 4

تَعۡرُجُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيۡهِ فِي يَوۡمٖ كَانَ مِقۡدَارُهُۥ خَمۡسِينَ أَلۡفَ سَنَةٖ

Mala’iku tare da Jibrilu suna hawa zuwa gare Shi a cikin wata rana (wadda) gwargwadonta yake daidai da shekara dubu hamsin



السورة: Suratul Jinn

الآية : 27

إِلَّا مَنِ ٱرۡتَضَىٰ مِن رَّسُولٖ فَإِنَّهُۥ يَسۡلُكُ مِنۢ بَيۡنِ يَدَيۡهِ وَمِنۡ خَلۡفِهِۦ رَصَدٗا

“Sai manzo da ya yarda da shi, shi kuma lalle Yakan sanya masa tsaro ta gabansa da ta bayansa[1]


1- Watau ta hanyar sa masa mala’iku masu tsaron sa domin kada shaixanu su samu kusantar sa.


السورة: Suratul Muddassir

الآية : 31

وَمَا جَعَلۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةٗۖ وَمَا جَعَلۡنَا عِدَّتَهُمۡ إِلَّا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيَسۡتَيۡقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَيَزۡدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِيمَٰنٗا وَلَا يَرۡتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ وَٱلۡكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَمَا يَعۡلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡبَشَرِ

Ba Mu kuwa sanya masu tsaron wutar ba sai mala’iku, ba Mu kuma sanya adadinsu ba sai don fitina ga waxanda suka kafirta, don kuma waxanda aka bai wa littafi su sami yaqini, waxanda kuma suka yi imani su qara imani, waxanda aka bai wa littafi da muminai kuma kada su yi tababa, don kuma waxanda suke da raunin imani a zukatansu da kuma kafirai su ce: “Me Allah Yake nufi da yin misali da wannan (adadin)?” Kamar haka Allah Yake vatar da wanda Ya ga dama, Yake kuma shiryar da wanda Ya ga dama. Ba kuma wanda ya san (yawan) rundunar Ubangijinka sai Shi. Ita (Saqara) kuma ba wata abu ba ce face wa’azi ga mutane



السورة: Suratun Naba’i

الآية : 38

يَوۡمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ صَفّٗاۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنۡ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَقَالَ صَوَابٗا

Ranar da Jibrilu da mala’iku za su tsaya sahu-sahu; (halittu) ba sa iya magana sai fa wanda (Allah) Mai rahama Ya yi wa izini, ya kuma faxi abin da ya dace[1]


1- Watau kalmar tauhidi.


السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 1

وَٱلنَّـٰزِعَٰتِ غَرۡقٗا

Na rantse da (mala’iku) masu cizgar (ran kafiri) mummunar cizga



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 2

وَٱلنَّـٰشِطَٰتِ نَشۡطٗا

Da kuma (mala’iku) masu zare (ran mumini) sassauqar zarewa



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 3

وَٱلسَّـٰبِحَٰتِ سَبۡحٗا

Da kuma (mala’iku) masu ninqaya (a sama don sauko da umarni) ninqaya mai tsananin sauri



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 4

فَٱلسَّـٰبِقَٰتِ سَبۡقٗا

Sannan da (mala’iku) masu matuqar rigegeniya (don zartar da umarnin Allah)



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 5

فَٱلۡمُدَبِّرَٰتِ أَمۡرٗا

Sannan da (mala’iku) masu tsara al’amura



السورة: Suratul Infixar

الآية : 10

وَإِنَّ عَلَيۡكُمۡ لَحَٰفِظِينَ

Kuma lalle akwai masu kula da ku[1]


1- Watau mala’iku.


السورة: Suratul Infixar

الآية : 11

كِرَامٗا كَٰتِبِينَ

Masu daraja marubuta



السورة: Suratul Infixar

الآية : 12

يَعۡلَمُونَ مَا تَفۡعَلُونَ

Suna sane da abin da kuke aikatawa



السورة: Suratul Fajr

الآية : 22

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا

Ubangijinka kuma Ya zo[1] tare da mala’iku sahu-sahu


1- Watau don yin hukunci a tsakanin bayinsa.


السورة: Suratul Alaq

الآية : 18

سَنَدۡعُ ٱلزَّبَانِيَةَ

Mu kuma lalle za Mu kirawo (mala’iku) zabaniyawa



السورة: Qadar

الآية : 4

تَنَزَّلُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ فِيهَا بِإِذۡنِ رَبِّهِم مِّن كُلِّ أَمۡرٖ

Mala’iku da Jibrilu suna ta saukowa da dukkanin al’amura a cikinsa da izinin Ubangijinsu