وَدَّ كَثِيرٞ مِّنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ لَوۡ يَرُدُّونَكُم مِّنۢ بَعۡدِ إِيمَٰنِكُمۡ كُفَّارًا حَسَدٗا مِّنۡ عِندِ أَنفُسِهِم مِّنۢ بَعۡدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُمُ ٱلۡحَقُّۖ فَٱعۡفُواْ وَٱصۡفَحُواْ حَتَّىٰ يَأۡتِيَ ٱللَّهُ بِأَمۡرِهِۦٓۗ إِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ
Da yawa daga cikin ma’abota littafi sun yi burin ina ma a ce su mayar da ku kafirai bayan imaninku, saboda hassada daga zukatansu, bayan kuma gaskiya ta bayyana a gare su. Don haka ku yi afuwa ku kawar da kai har sai Allah Ya zo da al’amarinsa. Lalle Allah Mai iko ne a kan komai
أَمۡ يَحۡسُدُونَ ٱلنَّاسَ عَلَىٰ مَآ ءَاتَىٰهُمُ ٱللَّهُ مِن فَضۡلِهِۦۖ فَقَدۡ ءَاتَيۡنَآ ءَالَ إِبۡرَٰهِيمَ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَءَاتَيۡنَٰهُم مُّلۡكًا عَظِيمٗا
Shin yanzu za su riqa yi wa mutane hassada ne a kan abin da Allah Ya ba su na falalarsa? To haqiqa Mun bai wa zurriyar gidan Ibrahimu Littafi da kuma hikima, kuma Mun ba su wani mulki mai girma
سَيَقُولُ ٱلۡمُخَلَّفُونَ إِذَا ٱنطَلَقۡتُمۡ إِلَىٰ مَغَانِمَ لِتَأۡخُذُوهَا ذَرُونَا نَتَّبِعۡكُمۡۖ يُرِيدُونَ أَن يُبَدِّلُواْ كَلَٰمَ ٱللَّهِۚ قُل لَّن تَتَّبِعُونَا كَذَٰلِكُمۡ قَالَ ٱللَّهُ مِن قَبۡلُۖ فَسَيَقُولُونَ بَلۡ تَحۡسُدُونَنَاۚ بَلۡ كَانُواْ لَا يَفۡقَهُونَ إِلَّا قَلِيلٗا
Waxanda suka qi fita tare da kai[1] za su ce, lokacin da kuka tafi zuwa wasu wuraren ganima don ku samo ta: “Ku bar mu mu bi ku”[2], suna nufin su musanya zancen Allah ne. Ka ce: “Ba za ku bi mu ba, da ma tuni haka Allah Ya faxa.” To za su ce: “A’a, kuna yi mana hassada ne kawai.” Ba haka ba ne, sun kasance ba sa fahimta ne sai ‘yan kaxan
1-  Watau suka fita tare da Annabi () zuwa Makka.
2-  Watau zuwa Khaibar.            
وَمِن شَرِّ حَاسِدٍ إِذَا حَسَدَ
“Da kuma sharrin mai hassada yayin da ya yi hassadar.”