السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 37

فَتَقَبَّلَهَا رَبُّهَا بِقَبُولٍ حَسَنٖ وَأَنۢبَتَهَا نَبَاتًا حَسَنٗا وَكَفَّلَهَا زَكَرِيَّاۖ كُلَّمَا دَخَلَ عَلَيۡهَا زَكَرِيَّا ٱلۡمِحۡرَابَ وَجَدَ عِندَهَا رِزۡقٗاۖ قَالَ يَٰمَرۡيَمُ أَنَّىٰ لَكِ هَٰذَاۖ قَالَتۡ هُوَ مِنۡ عِندِ ٱللَّهِۖ إِنَّ ٱللَّهَ يَرۡزُقُ مَن يَشَآءُ بِغَيۡرِ حِسَابٍ

Sai Ubangijinta Ya karve ta da kyakkyawar karva, kuma Ya yi mata kyakkyawar tarbiyya, kuma Ya danqa renonta a hannun Zakariyya; duk lokacin da Zakariyya ya shiga wurinta a xakin ibada, sai ya sami abinci a wurinta, sai ya ce: “Ya ke Maryamu, wannan daga ina kika samu?” Sai ta ce: “Wannan daga Allah ne; lalle Allah Yana arzurta wanda Ya ga dama ba tare da lissafi ba.”



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 38

هُنَالِكَ دَعَا زَكَرِيَّا رَبَّهُۥۖ قَالَ رَبِّ هَبۡ لِي مِن لَّدُنكَ ذُرِّيَّةٗ طَيِّبَةًۖ إِنَّكَ سَمِيعُ ٱلدُّعَآءِ

A wannan lokacin sai Zakariyya ya roqi Ubangijinsa, ya ce: “Ya Ubangijina, Ka ba ni zurriyya ta gari daga gare Ka, lalle Kai Mai amsa roqo ne.”



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 39

فَنَادَتۡهُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَهُوَ قَآئِمٞ يُصَلِّي فِي ٱلۡمِحۡرَابِ أَنَّ ٱللَّهَ يُبَشِّرُكَ بِيَحۡيَىٰ مُصَدِّقَۢا بِكَلِمَةٖ مِّنَ ٱللَّهِ وَسَيِّدٗا وَحَصُورٗا وَنَبِيّٗا مِّنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Sai mala’iku suka kira shi, lokacin yana tsaye yana salla a cikin xakin ibada, (suka ce): “Lalle Allah Yana yi maka albishir da Yahya, wanda yake mai gaskatawa da wata kalma daga Allah, kuma zai zama shugaba, kuma mai tsare kansa daga mata, kuma Annabi daga cikin salihan bayi.”



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 40

قَالَ رَبِّ أَنَّىٰ يَكُونُ لِي غُلَٰمٞ وَقَدۡ بَلَغَنِيَ ٱلۡكِبَرُ وَٱمۡرَأَتِي عَاقِرٞۖ قَالَ كَذَٰلِكَ ٱللَّهُ يَفۡعَلُ مَا يَشَآءُ

Ya ce: “Ya Ubangijina, ta yaya zan sami xa, ga shi tsufa ya riga ya cim mini, kuma ga shi matata juya ce?” Sai ya ce: “Kamar haka ne Allah Yake aikata abin da Ya ga dama.”



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 41

قَالَ رَبِّ ٱجۡعَل لِّيٓ ءَايَةٗۖ قَالَ ءَايَتُكَ أَلَّا تُكَلِّمَ ٱلنَّاسَ ثَلَٰثَةَ أَيَّامٍ إِلَّا رَمۡزٗاۗ وَٱذۡكُر رَّبَّكَ كَثِيرٗا وَسَبِّحۡ بِٱلۡعَشِيِّ وَٱلۡإِبۡكَٰرِ

Ya ce: “Ya Ubangijina, Ka sanya mini wata alama.” Ya ce: “Alamarka ita ce ka kasa yi wa mutane magana yini uku sai dai da nuni. Kuma ka ambaci Ubangijinka ambato mai yawa, kuma ka yi tasbihi yammaci da safiya.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 85

وَزَكَرِيَّا وَيَحۡيَىٰ وَعِيسَىٰ وَإِلۡيَاسَۖ كُلّٞ مِّنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Da Zakariyya da Yahaya da Isa da Iliyasu; kowanne daga cikinsu yana cikin salihan bayi



السورة: Suratu Maryam

الآية : 2

ذِكۡرُ رَحۡمَتِ رَبِّكَ عَبۡدَهُۥ زَكَرِيَّآ

(Wannan) ambaton rahamar Ubangijinka ne (da Ya yi wa) Bawansa Zakariyya



السورة: Suratu Maryam

الآية : 3

إِذۡ نَادَىٰ رَبَّهُۥ نِدَآءً خَفِيّٗا

Lokacin da ya kira Ubangijinsa (ya roqe Shi) cikin asiri



السورة: Suratu Maryam

الآية : 4

قَالَ رَبِّ إِنِّي وَهَنَ ٱلۡعَظۡمُ مِنِّي وَٱشۡتَعَلَ ٱلرَّأۡسُ شَيۡبٗا وَلَمۡ أَكُنۢ بِدُعَآئِكَ رَبِّ شَقِيّٗا

Ya ce: “Ya Ubangiji lalle qasusuwana sun yi rauni, kaina kuma ya yi fari fat da furfura, Ubangijina ban kuma zama mai tavewa ba game da roqon Ka



السورة: Suratu Maryam

الآية : 5

وَإِنِّي خِفۡتُ ٱلۡمَوَٰلِيَ مِن وَرَآءِي وَكَانَتِ ٱمۡرَأَتِي عَاقِرٗا فَهَبۡ لِي مِن لَّدُنكَ وَلِيّٗا

“Kuma lalle ni na ji tsoron dangina a bayana[1], matata kuma ga ta bakarara ce, saboda haka Ka yi mini baiwa daga gare Ka ta (xa) majivinci


1- Watau kada su watsar da kulawa da addini, su shagala da neman abincinsu.


السورة: Suratu Maryam

الآية : 6

يَرِثُنِي وَيَرِثُ مِنۡ ءَالِ يَعۡقُوبَۖ وَٱجۡعَلۡهُ رَبِّ رَضِيّٗا

“(Wanda) zai gaje ni[1] ya kuma gaji iyalan Ya’aqub; Ubangijina kuma Ka sanya shi yardajje (a wurinka).”


1- Watau ya gaji ilimi da annabta da shugabantar gudanar da harkokin addini.


السورة: Suratu Maryam

الآية : 7

يَٰزَكَرِيَّآ إِنَّا نُبَشِّرُكَ بِغُلَٰمٍ ٱسۡمُهُۥ يَحۡيَىٰ لَمۡ نَجۡعَل لَّهُۥ مِن قَبۡلُ سَمِيّٗا

(Aka ce): Ya Zakariyya, lalle Muna yi maka albishir da samun xa, sunansa Yahya, ba Mu kuwa sanya wa wani sunan ba gabaninsa



السورة: Suratu Maryam

الآية : 8

قَالَ رَبِّ أَنَّىٰ يَكُونُ لِي غُلَٰمٞ وَكَانَتِ ٱمۡرَأَتِي عَاقِرٗا وَقَدۡ بَلَغۡتُ مِنَ ٱلۡكِبَرِ عِتِيّٗا

Ya ce: “Ubangijina ta qaqa zan samu xa, alhali kuwa matata ta zamanto bakarara ce, ni kuma ga shi na tsufa tukuf”



السورة: Suratu Maryam

الآية : 9

قَالَ كَذَٰلِكَ قَالَ رَبُّكَ هُوَ عَلَيَّ هَيِّنٞ وَقَدۡ خَلَقۡتُكَ مِن قَبۡلُ وَلَمۡ تَكُ شَيۡـٔٗا

Ya ce: “Kamar haka Ubangijinka Ya faxa (cewa): ‘Shi (wannan) mai sauqi ne a wurina, don kuwa haqiqa Na halicce ka alhalin ba ka zama komai ba.’”



السورة: Suratu Maryam

الآية : 10

قَالَ رَبِّ ٱجۡعَل لِّيٓ ءَايَةٗۖ قَالَ ءَايَتُكَ أَلَّا تُكَلِّمَ ٱلنَّاسَ ثَلَٰثَ لَيَالٖ سَوِيّٗا

Ya ce: “Ubangijina Ka sanya mini wata alama.” Sai (Allah) Ya ce: “Alamarka ita ce ka kasa yi wa mutane magana (tsawon) kwana uku daidai.”



السورة: Suratu Maryam

الآية : 11

فَخَرَجَ عَلَىٰ قَوۡمِهِۦ مِنَ ٱلۡمِحۡرَابِ فَأَوۡحَىٰٓ إِلَيۡهِمۡ أَن سَبِّحُواْ بُكۡرَةٗ وَعَشِيّٗا

Sannan (Zakariyya) ya fito wa mutanensa daga wurin ibada ya yi musu ishara cewa: “Ku yi tasbihi safe da maraice.”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 89

وَزَكَرِيَّآ إِذۡ نَادَىٰ رَبَّهُۥ رَبِّ لَا تَذَرۡنِي فَرۡدٗا وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلۡوَٰرِثِينَ

(Ka tuna) kuma Zakariya’u lokacin da ya roqi Ubangijinsa (cewa): “Ya Ubangijina, kada Ka bar ni ni kaxai (ba magaji), Kai ne kuwa Fiyayyen magada.”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 90

فَٱسۡتَجَبۡنَا لَهُۥ وَوَهَبۡنَا لَهُۥ يَحۡيَىٰ وَأَصۡلَحۡنَا لَهُۥ زَوۡجَهُۥٓۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ يُسَٰرِعُونَ فِي ٱلۡخَيۡرَٰتِ وَيَدۡعُونَنَا رَغَبٗا وَرَهَبٗاۖ وَكَانُواْ لَنَا خَٰشِعِينَ

Sai Muka amsa masa Muka ba shi Yahya, Muka kuma gyara masa (mahaifar) matarsa. Lallai su sun kasance suna gaggawa wajen yin alherai, suna kuma roqon Mu suna masu kwaxayin (rahamarmu) masu kuma tsoron (azabarmu), sun kuma zamanto masu qasqantar da kai gare Mu