السورة: Suratul Insan

الآية : 25

وَٱذۡكُرِ ٱسۡمَ رَبِّكَ بُكۡرَةٗ وَأَصِيلٗا

Ka kuma ambaci sunan Ubangijinka safe da yamma



السورة: Suratul Insan

الآية : 26

وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَٱسۡجُدۡ لَهُۥ وَسَبِّحۡهُ لَيۡلٗا طَوِيلًا

Da daddare kuma sai ka yi sujjada a gare Shi, ka kuma yi nafiloli saboda Shi a tsawon dare



السورة: Suratul Bayyina

الآية : 5

وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ حُنَفَآءَ وَيُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤۡتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَذَٰلِكَ دِينُ ٱلۡقَيِّمَةِ

Ba a kuma umarce su ba sai don su bauta wa Allah suna masu tsantsanta addini gare Shi, suna masu kauce wa varna, suna kuma tsayar da salla, kuma suna ba da zakka. Wannan kuwa shi ne addinin miqaqqiyar hanya



السورة: Suratu Quraish

الآية : 3

فَلۡيَعۡبُدُواْ رَبَّ هَٰذَا ٱلۡبَيۡتِ

To sai su bauta wa Ubangijin wannan Xakin[1]


1- Watau Xakin Ka’aba mai alfarma.


السورة: Suratu Quraish

الآية : 4

ٱلَّذِيٓ أَطۡعَمَهُم مِّن جُوعٖ وَءَامَنَهُم مِّنۡ خَوۡفِۭ

Wanda Ya ciyar da su daga yunwa, Ya kuma amintar da su daga tsoro



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 1

قُلۡ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡكَٰفِرُونَ

Ka ce: “Ya ku waxannan kafirai



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 2

لَآ أَعۡبُدُ مَا تَعۡبُدُونَ

“Ba zan bauta wa abin da kuke bauta wa ba



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 3

وَلَآ أَنتُمۡ عَٰبِدُونَ مَآ أَعۡبُدُ

“Ku kuma ba masu bautar abin da nake bauta wa ba ne



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 4

وَلَآ أَنَا۠ عَابِدٞ مَّا عَبَدتُّمۡ

“Ni kuma ba mai bauta wa abin da kuka bauta wa ba ne



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 5

وَلَآ أَنتُمۡ عَٰبِدُونَ مَآ أَعۡبُدُ

“Ku ma ba za ku bauta wa abin da nake bauta wa ba



السورة: Suratul Kafirun

الآية : 6

لَكُمۡ دِينُكُمۡ وَلِيَ دِينِ

“Addininku na gare ku, ni ma kuma addinina na gare ni[1].”


1- Annabi () ya ga wani yana karanta wannan Surar sai ya ce: “Amma dai wannan haqiqa ya kuvuta daga shirka”.