وَٱذۡكُرِ ٱسۡمَ رَبِّكَ بُكۡرَةٗ وَأَصِيلٗا
Ka kuma ambaci sunan Ubangijinka safe da yamma
وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَٱسۡجُدۡ لَهُۥ وَسَبِّحۡهُ لَيۡلٗا طَوِيلًا
Da daddare kuma sai ka yi sujjada a gare Shi, ka kuma yi nafiloli saboda Shi a tsawon dare
وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ حُنَفَآءَ وَيُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤۡتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَذَٰلِكَ دِينُ ٱلۡقَيِّمَةِ
Ba a kuma umarce su ba sai don su bauta wa Allah suna masu tsantsanta addini gare Shi, suna masu kauce wa varna, suna kuma tsayar da salla, kuma suna ba da zakka. Wannan kuwa shi ne addinin miqaqqiyar hanya
فَلۡيَعۡبُدُواْ رَبَّ هَٰذَا ٱلۡبَيۡتِ
To sai su bauta wa Ubangijin wannan Xakin[1]
1- Watau Xakin Ka’aba mai alfarma.
ٱلَّذِيٓ أَطۡعَمَهُم مِّن جُوعٖ وَءَامَنَهُم مِّنۡ خَوۡفِۭ
Wanda Ya ciyar da su daga yunwa, Ya kuma amintar da su daga tsoro
قُلۡ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡكَٰفِرُونَ
Ka ce: “Ya ku waxannan kafirai
لَآ أَعۡبُدُ مَا تَعۡبُدُونَ
“Ba zan bauta wa abin da kuke bauta wa ba
وَلَآ أَنتُمۡ عَٰبِدُونَ مَآ أَعۡبُدُ
“Ku kuma ba masu bautar abin da nake bauta wa ba ne
وَلَآ أَنَا۠ عَابِدٞ مَّا عَبَدتُّمۡ
“Ni kuma ba mai bauta wa abin da kuka bauta wa ba ne
وَلَآ أَنتُمۡ عَٰبِدُونَ مَآ أَعۡبُدُ
“Ku ma ba za ku bauta wa abin da nake bauta wa ba
لَكُمۡ دِينُكُمۡ وَلِيَ دِينِ
“Addininku na gare ku, ni ma kuma addinina na gare ni[1].”
1- Annabi () ya ga wani yana karanta wannan Surar sai ya ce: “Amma dai wannan haqiqa ya kuvuta daga shirka”.