السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 146

أَتُتۡرَكُونَ فِي مَا هَٰهُنَآ ءَامِنِينَ

“Yanzu (zatonku) za a bar ku ne cikin abin da yake a nan (duniya) cikin kwanciyar hankali?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 147

فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

“(Watau) a cikin gonaki da idandunan ruwa?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 148

وَزُرُوعٖ وَنَخۡلٖ طَلۡعُهَا هَضِيمٞ

“Da shuke-shuke da dabinai masu taushin ‘ya’ya?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 149

وَتَنۡحِتُونَ مِنَ ٱلۡجِبَالِ بُيُوتٗا فَٰرِهِينَ

“Kuma kuna fafe duwatsu kuna yin gidaje kuna masu nuna qwarewa?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 150

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 151

وَلَا تُطِيعُوٓاْ أَمۡرَ ٱلۡمُسۡرِفِينَ

“Kada kuma ku bi umarnin mavarnata



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 152

ٱلَّذِينَ يُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا يُصۡلِحُونَ

“Waxanda suke varna a bayan qasa, kuma ba sa gyara.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 153

قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ

Suka ce: “Lalle kai kana daga waxanda aka sihirce ne kawai



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 154

مَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا فَأۡتِ بِـَٔايَةٍ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

“Kai ba kowa ba ne sai mutum kamarmu, to ka zo mana da aya idan ka kasance daga masu gaskiya.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 155

قَالَ هَٰذِهِۦ نَاقَةٞ لَّهَا شِرۡبٞ وَلَكُمۡ شِرۡبُ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ

(Salihu) ya ce: “Wannan taguwa ce[1], tana da (ranar) shanta ku ma kuna da rana sananniya ta shanku


1- Watau a matsayin mu’ujiza ga Annabi Salihu ().


السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 156

وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٖ فَيَأۡخُذَكُمۡ عَذَابُ يَوۡمٍ عَظِيمٖ

“Kada kuwa ku shafe ta da mugun abu, sai azabar wani yini mai girma ta kama ku.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 157

فَعَقَرُوهَا فَأَصۡبَحُواْ نَٰدِمِينَ

Sai suka soke ta, sai kuwa suka wayi gari suna masu nadama



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 158

فَأَخَذَهُمُ ٱلۡعَذَابُۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Sai azaba ta kama su. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 159

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



السورة: Suratun Namli

الآية : 45

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَآ إِلَىٰ ثَمُودَ أَخَاهُمۡ صَٰلِحًا أَنِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ فَإِذَا هُمۡ فَرِيقَانِ يَخۡتَصِمُونَ

Haqiqa kuma Mun aiko wa Samudawa xan’uwansu Salihu da cewa: “Ku bauta wa Allah,” sai ga su sun rabu qungiyoyi biyu[1] suna jayayya


1- Watau qungiya ta farko su ne waxanda suka yi imani da Annabi Salihu, qungiya ta biyu su ne waxanda suka kafirce masa.


السورة: Suratun Namli

الآية : 46

قَالَ يَٰقَوۡمِ لِمَ تَسۡتَعۡجِلُونَ بِٱلسَّيِّئَةِ قَبۡلَ ٱلۡحَسَنَةِۖ لَوۡلَا تَسۡتَغۡفِرُونَ ٱللَّهَ لَعَلَّكُمۡ تُرۡحَمُونَ

Ya ce: “Ya ku mutanena, don me kuke neman gaggautowar mummunan sakamako tun gabanin kyakkyawa[1]? Don me ba za ku nemi gafarar Allah ba don a ji qan ku.”


1- Watau suna neman a kawo musu azaba, maimakon su roqi rahamar Allah.


السورة: Suratun Namli

الآية : 47

قَالُواْ ٱطَّيَّرۡنَا بِكَ وَبِمَن مَّعَكَۚ قَالَ طَـٰٓئِرُكُمۡ عِندَ ٱللَّهِۖ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٞ تُفۡتَنُونَ

Sai suka ce: “Mu mun camfa ka kai da waxanda suke tare da kai.” Sai ya ce: “Camfinku na ga Allah. A’a, ku dai mutane ne da ake jarraba ku.”



السورة: Suratun Namli

الآية : 48

وَكَانَ فِي ٱلۡمَدِينَةِ تِسۡعَةُ رَهۡطٖ يُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا يُصۡلِحُونَ

A cikin birnin kuma akwai wani gungu na mutum tara waxanda suke varna a bayan qasa kuma ba sa gyara



السورة: Suratun Namli

الآية : 49

قَالُواْ تَقَاسَمُواْ بِٱللَّهِ لَنُبَيِّتَنَّهُۥ وَأَهۡلَهُۥ ثُمَّ لَنَقُولَنَّ لِوَلِيِّهِۦ مَا شَهِدۡنَا مَهۡلِكَ أَهۡلِهِۦ وَإِنَّا لَصَٰدِقُونَ

Sai suka ce wa (juna): “Ku rantse da Allah cewa, lalle za mu kashe shi cikin dare shi da iyalinsa, sannan za mu faxa wa mai neman jininsa cewa, ba mu halarci wurin kashe iyalinsa ba, kuma lalle mu masu gaskiya ne.”



السورة: Suratun Namli

الآية : 50

وَمَكَرُواْ مَكۡرٗا وَمَكَرۡنَا مَكۡرٗا وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

Kuma suka shirya makirci, Mu kuma Muka shirya rusa makircinsu alhali kuwa su ba su sani ba



السورة: Suratun Namli

الآية : 51

فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ مَكۡرِهِمۡ أَنَّا دَمَّرۡنَٰهُمۡ وَقَوۡمَهُمۡ أَجۡمَعِينَ

Sai ka duba ka ga yadda qarshen makircinsu ya zama, watau Mun hallakar da su tare da mutanensu baki xaya



السورة: Suratun Namli

الآية : 52

فَتِلۡكَ بُيُوتُهُمۡ خَاوِيَةَۢ بِمَا ظَلَمُوٓاْۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّقَوۡمٖ يَعۡلَمُونَ

To ga gidajensu can a rugurguje babu kowa saboda zaluncinsu. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya ga mutanen da suke ganewa



السورة: Suratun Namli

الآية : 53

وَأَنجَيۡنَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَكَانُواْ يَتَّقُونَ

Muka kuma tserar da waxanda suka yi imani, suka kuma kasance suna kiyaye dokokin Allah



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 38

وَعَادٗا وَثَمُودَاْ وَقَد تَّبَيَّنَ لَكُم مِّن مَّسَٰكِنِهِمۡۖ وَزَيَّنَ لَهُمُ ٱلشَّيۡطَٰنُ أَعۡمَٰلَهُمۡ فَصَدَّهُمۡ عَنِ ٱلسَّبِيلِ وَكَانُواْ مُسۡتَبۡصِرِينَ

Kuma (Mun hallaka) Adawa da Samudawa, haqiqa (abin da ya faru a gare su) ya bayyana gare ku a fili a gidajensu; kuma Shaixan ya qawata musu ayyukansu, sai ya kange su daga hanya (madaidaiciya), sun kuma kasance masu gani da basirarsu (amma suka zavi vata)



السورة: Suratu Sad

الآية : 13

وَثَمُودُ وَقَوۡمُ لُوطٖ وَأَصۡحَٰبُ لۡـَٔيۡكَةِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلۡأَحۡزَابُ

Da kuma Samudawa da mutanen Luxu da mutanen Sarqaqiya[1]. Waxannan su ne al’ummun


1- Su ne mutanen Annabi Shu’aibu ().


السورة: Suratu Ghafir

الآية : 31

مِثۡلَ دَأۡبِ قَوۡمِ نُوحٖ وَعَادٖ وَثَمُودَ وَٱلَّذِينَ مِنۢ بَعۡدِهِمۡۚ وَمَا ٱللَّهُ يُرِيدُ ظُلۡمٗا لِّلۡعِبَادِ

“Kamar misalin al’adar mutanen Nuhu da Adawa da Samudawa da kuma waxanda suka zo bayansu. Allah kuwa ba Ya nufin zalunci ga bayi



السورة: Suratu Fussilat

الآية : 13

فَإِنۡ أَعۡرَضُواْ فَقُلۡ أَنذَرۡتُكُمۡ صَٰعِقَةٗ مِّثۡلَ صَٰعِقَةِ عَادٖ وَثَمُودَ

To idan suka bijire sai ka ce: “Na tsoratar da ku da tsawa irin tsawar Adawa da Samudawa



السورة: Suratu Fussilat

الآية : 17

وَأَمَّا ثَمُودُ فَهَدَيۡنَٰهُمۡ فَٱسۡتَحَبُّواْ ٱلۡعَمَىٰ عَلَى ٱلۡهُدَىٰ فَأَخَذَتۡهُمۡ صَٰعِقَةُ ٱلۡعَذَابِ ٱلۡهُونِ بِمَا كَانُواْ يَكۡسِبُونَ

Amma Samudawa kuma sai Muka nuna musu hanyar shiriya, sai suka zavi vata a kan shiriya, sai tsawar azabar wulaqanci ta kama su saboda abin da suka kasance suna tsuwurwuta



السورة: Suratu Qaf 

الآية : 12

كَذَّبَتۡ قَبۡلَهُمۡ قَوۡمُ نُوحٖ وَأَصۡحَٰبُ ٱلرَّسِّ وَثَمُودُ

Mutanen Nuhu da ma’abota rijiyar Rassu da Samudawa (duka) sun qaryata (annabawa) a gabaninsu (watau mutanen Makka)



السورة: Suratuz Zariyat

الآية : 43

وَفِي ثَمُودَ إِذۡ قِيلَ لَهُمۡ تَمَتَّعُواْ حَتَّىٰ حِينٖ

Kuma game da Samudawa (akwai aya), lokacin da aka ce da su: “Ku ji daxi zuwa wani xan lokaci[1].”


1- Watau wa’adin kwana uku kacal.