السورة: Suratul Qalam

الآية : 27

بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ

“A’a, mu dai an hana mu ne kawai.”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 28

قَالَ أَوۡسَطُهُمۡ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ لَوۡلَا تُسَبِّحُونَ

Sai wanda ya fi su kirki ya ce: “Ban gaya muku ya kamata ku tsarkake Allah ba?”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 29

قَالُواْ سُبۡحَٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ

Suka ce, “Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu, lalle mu mun kasance azzalumai.”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 30

فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَلَٰوَمُونَ

Sai sashinsu ya fuskanci sashi suna zargin juna



السورة: Suratul Qalam

الآية : 31

قَالُواْ يَٰوَيۡلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَٰغِينَ

Suka ce: “Kaiconmu, lalle mu mun kasance masu shisshigi



السورة: Suratul Qalam

الآية : 32

عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبۡدِلَنَا خَيۡرٗا مِّنۡهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ

“Tsammanin Ubangijinmu zai musanya mana wadda ta fi ta, lalle mu masu kwaxayi ne a wurin Ubangijinmu[1].”


1- Watau zai ba su wata gonar da ta fi tasu, suna kuma fatan zai yi musu afuwa ya yafe musu kurakuransu.


السورة: Suratul Qalam

الآية : 33

كَذَٰلِكَ ٱلۡعَذَابُۖ وَلَعَذَابُ ٱلۡأٓخِرَةِ أَكۡبَرُۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ

Kamar haka ne azaba take tabbata; kuma tabbas azabar lahira ta fi girma. Da sun kasance sun san haka