السورة: Suratu Yasin

الآية : 32

وَإِن كُلّٞ لَّمَّا جَمِيعٞ لَّدَيۡنَا مُحۡضَرُونَ

Kuma duk gaba xayansu wurinmu za a tattara su



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 28

وَقَالَ رَجُلٞ مُّؤۡمِنٞ مِّنۡ ءَالِ فِرۡعَوۡنَ يَكۡتُمُ إِيمَٰنَهُۥٓ أَتَقۡتُلُونَ رَجُلًا أَن يَقُولَ رَبِّيَ ٱللَّهُ وَقَدۡ جَآءَكُم بِٱلۡبَيِّنَٰتِ مِن رَّبِّكُمۡۖ وَإِن يَكُ كَٰذِبٗا فَعَلَيۡهِ كَذِبُهُۥۖ وَإِن يَكُ صَادِقٗا يُصِبۡكُم بَعۡضُ ٱلَّذِي يَعِدُكُمۡۖ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي مَنۡ هُوَ مُسۡرِفٞ كَذَّابٞ

Kuma wani mutum mumini daga dangin Fir’auna wanda yake voye imaninsa ya ce: “Yanzu kwa kashe mutum don ya ce ‘Allah ne Ubangijina’, kuma alhalin ya zo muku da hujjoji bayyanannu daga Ubangijinku? Idan ya zama maqaryaci ne to laifin qaryarsa yana kansa; idan kuwa ya zama mai gaskiya, to wani abu daga abin da yake yi muku gargaxinsa zai same ku. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake shi mai yawan varna ne, maqaryaci



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 29

يَٰقَوۡمِ لَكُمُ ٱلۡمُلۡكُ ٱلۡيَوۡمَ ظَٰهِرِينَ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَمَن يَنصُرُنَا مِنۢ بَأۡسِ ٱللَّهِ إِن جَآءَنَاۚ قَالَ فِرۡعَوۡنُ مَآ أُرِيكُمۡ إِلَّا مَآ أَرَىٰ وَمَآ أَهۡدِيكُمۡ إِلَّا سَبِيلَ ٱلرَّشَادِ

“Ya ku mutanena, a yau ku ne masu mulki masu qarfi a bayan qasa, to wane ne zai kare mu daga azabar Allah idan ta zo mana?” Fir’auna ya ce: “Ba abin da nake nuna muku sai abin da na gani (shi ne daidai), kuma hanyar shiriya kaxai nake nuna muku.”



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 30

وَقَالَ ٱلَّذِيٓ ءَامَنَ يَٰقَوۡمِ إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُم مِّثۡلَ يَوۡمِ ٱلۡأَحۡزَابِ

Sai kuma wannan da ya yi imani ya ce: “Ya ku mutanena, lalle ni ina jiye muku tsoron irin ranar gangamin qungiyoyin (kafirai)



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 31

مِثۡلَ دَأۡبِ قَوۡمِ نُوحٖ وَعَادٖ وَثَمُودَ وَٱلَّذِينَ مِنۢ بَعۡدِهِمۡۚ وَمَا ٱللَّهُ يُرِيدُ ظُلۡمٗا لِّلۡعِبَادِ

“Kamar misalin al’adar mutanen Nuhu da Adawa da Samudawa da kuma waxanda suka zo bayansu. Allah kuwa ba Ya nufin zalunci ga bayi



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 32

وَيَٰقَوۡمِ إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ يَوۡمَ ٱلتَّنَادِ

“Kuma ya ku mutanena, lalle ni ina jiye muku tsoron ranar kiraye-kirayen juna (ranar alqiyama)[1]


1- Watau mutane za su riqa kiran junansu saboda dangantaka ta jini suna neman alfarma.


السورة: Suratu Ghafir

الآية : 33

يَوۡمَ تُوَلُّونَ مُدۡبِرِينَ مَا لَكُم مِّنَ ٱللَّهِ مِنۡ عَاصِمٖۗ وَمَن يُضۡلِلِ ٱللَّهُ فَمَا لَهُۥ مِنۡ هَادٖ

“Ranar da za ku juya kuna masu ba da baya, ba ku da wani mai kare ku daga Allah. Duk kuma wanda Allah Ya vatar to ba shi da wani mai shiryarwa.”



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 34

وَلَقَدۡ جَآءَكُمۡ يُوسُفُ مِن قَبۡلُ بِٱلۡبَيِّنَٰتِ فَمَا زِلۡتُمۡ فِي شَكّٖ مِّمَّا جَآءَكُم بِهِۦۖ حَتَّىٰٓ إِذَا هَلَكَ قُلۡتُمۡ لَن يَبۡعَثَ ٱللَّهُ مِنۢ بَعۡدِهِۦ رَسُولٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَنۡ هُوَ مُسۡرِفٞ مُّرۡتَابٌ

Haqiqa kuma Yusufu ya zo muku da (hujjoji) bayyanannu tun kafin (zuwan Musa), to ba ku gushe kuna kokwanton abin da ya zo muku da shi ba, har yayin da ya mutu sai kuka ce: “Allah ba zai sake aiko da wani manzo bayansa ba.” Kamar haka ne Allah Yake vatar da duk wanda shi mai varna ne, mai shakka



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 35

ٱلَّذِينَ يُجَٰدِلُونَ فِيٓ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ بِغَيۡرِ سُلۡطَٰنٍ أَتَىٰهُمۡۖ كَبُرَ مَقۡتًا عِندَ ٱللَّهِ وَعِندَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْۚ كَذَٰلِكَ يَطۡبَعُ ٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ قَلۡبِ مُتَكَبِّرٖ جَبَّارٖ

Waxanda suke yin jayayya game da ayoyin Allah ba tare da wata hujja da ta zo musu ba; qyamar (wannan) a wurin Allah da wurin waxanda suka yi imani ta girmama. Kamar haka ne Allah Yake toshe zuciyar duk wani mai girman kai, mai tsaurin rai



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 36

وَقَالَ فِرۡعَوۡنُ يَٰهَٰمَٰنُ ٱبۡنِ لِي صَرۡحٗا لَّعَلِّيٓ أَبۡلُغُ ٱلۡأَسۡبَٰبَ

Fir’auna kuma ya ce: “Ya Hamana, ka gina min dogon gini ko na kai ga hanyoyi



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 37

أَسۡبَٰبَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ فَأَطَّلِعَ إِلَىٰٓ إِلَٰهِ مُوسَىٰ وَإِنِّي لَأَظُنُّهُۥ كَٰذِبٗاۚ وَكَذَٰلِكَ زُيِّنَ لِفِرۡعَوۡنَ سُوٓءُ عَمَلِهِۦ وَصُدَّ عَنِ ٱلسَّبِيلِۚ وَمَا كَيۡدُ فِرۡعَوۡنَ إِلَّا فِي تَبَابٖ

“(Watau) hanyoyin (da ke kaiwa zuwa) sammai sai in gano Ubangijin Musa, lalle kuma ni ina tsammaninsa maqaryaci ne.” Kamar haka kuma aka qawata wa Fir’auna mummunan aikinsa aka kuma kange shi daga hanyar (gaskiya). Makircin Fir’auna kuwa ba a komai yake ba sai cikin halaka



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 38

وَقَالَ ٱلَّذِيٓ ءَامَنَ يَٰقَوۡمِ ٱتَّبِعُونِ أَهۡدِكُمۡ سَبِيلَ ٱلرَّشَادِ

Sai (mutumin nan) wanda ya yi imani ya ce: “Ya ku mutanena, ku bi ni in nuna muku hanyar shiriya



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 39

يَٰقَوۡمِ إِنَّمَا هَٰذِهِ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَا مَتَٰعٞ وَإِنَّ ٱلۡأٓخِرَةَ هِيَ دَارُ ٱلۡقَرَارِ

“Ya ku mutanena, lalle wannan rayuwar ta duniya xan jin daxi ne, kuma lalle lahira ita ce gidan tabbata



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 40

مَنۡ عَمِلَ سَيِّئَةٗ فَلَا يُجۡزَىٰٓ إِلَّا مِثۡلَهَاۖ وَمَنۡ عَمِلَ صَٰلِحٗا مِّن ذَكَرٍ أَوۡ أُنثَىٰ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَأُوْلَـٰٓئِكَ يَدۡخُلُونَ ٱلۡجَنَّةَ يُرۡزَقُونَ فِيهَا بِغَيۡرِ حِسَابٖ

“Wanda ya aikata wani mummunan aiki, to ba za a saka masa ba sai da kwatankwacinsa, wanda kuwa ya aikata wani kyakkyawan aiki, namiji ne ko mace alhali shi yana mumini, to waxannan za su shiga Aljanna, a riqa arzuta su a cikinta ba tare da lissafi ba



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 41

۞وَيَٰقَوۡمِ مَا لِيٓ أَدۡعُوكُمۡ إِلَى ٱلنَّجَوٰةِ وَتَدۡعُونَنِيٓ إِلَى ٱلنَّارِ

“Kuma ya ku mutanena, me ya sa ne nake kiranku zuwa ga tsira, ku kuma kuke kira na zuwa wuta?



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 42

تَدۡعُونَنِي لِأَكۡفُرَ بِٱللَّهِ وَأُشۡرِكَ بِهِۦ مَا لَيۡسَ لِي بِهِۦ عِلۡمٞ وَأَنَا۠ أَدۡعُوكُمۡ إِلَى ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡغَفَّـٰرِ

“Kuna kira na da in kafirce wa Allah, in kuma tara Shi da abin da ba ni da wani sani a kansa, ni kuma ina kiran ku zuwa Mabuwayi, Mai yawan gafara?



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 43

لَا جَرَمَ أَنَّمَا تَدۡعُونَنِيٓ إِلَيۡهِ لَيۡسَ لَهُۥ دَعۡوَةٞ فِي ٱلدُّنۡيَا وَلَا فِي ٱلۡأٓخِرَةِ وَأَنَّ مَرَدَّنَآ إِلَى ٱللَّهِ وَأَنَّ ٱلۡمُسۡرِفِينَ هُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِ

“Ba shakka abin da kuke kira na zuwa gare shi ba shi da wani kira karvavve a duniya ko a lahira, kuma lalle makomarmu zuwa ga Allah ne, mavarnata kuma tabbas su ne ‘yan wuta



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 44

فَسَتَذۡكُرُونَ مَآ أَقُولُ لَكُمۡۚ وَأُفَوِّضُ أَمۡرِيٓ إِلَى ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ بَصِيرُۢ بِٱلۡعِبَادِ

“To ba da daxewa ba za ku tuna abin da nake gaya muku. Ina kuma miqa al’amarina zuwa ga Allah. Lalle Allah Mai ganin bayi ne.”



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 45

فَوَقَىٰهُ ٱللَّهُ سَيِّـَٔاتِ مَا مَكَرُواْۖ وَحَاقَ بِـَٔالِ فِرۡعَوۡنَ سُوٓءُ ٱلۡعَذَابِ

Sai Allah Ya kiyaye shi (sakamakon) mummunan abin da suka shirya; kuma mummunar azaba ta saukar wa mutanen Fir’auna



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 46

ٱلنَّارُ يُعۡرَضُونَ عَلَيۡهَا غُدُوّٗا وَعَشِيّٗاۚ وَيَوۡمَ تَقُومُ ٱلسَّاعَةُ أَدۡخِلُوٓاْ ءَالَ فِرۡعَوۡنَ أَشَدَّ ٱلۡعَذَابِ

(Ita ce) wuta da za a riqa bijirar da su a gare ta safe da yamma; Ranar tashin alqiyama kuma za a ce: “Ku shigar da mutanen Fir’auna mafi tsananin azaba



السورة: Suratul Qalam

الآية : 17

إِنَّا بَلَوۡنَٰهُمۡ كَمَا بَلَوۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡجَنَّةِ إِذۡ أَقۡسَمُواْ لَيَصۡرِمُنَّهَا مُصۡبِحِينَ

Lalle Mu Mun jarrabe su (wato mutanen Makka) kamar yadda Muka jarrabi ma’abota gona, lokacin da suka rantse cewa, lalle tabbas za su girbe ta da asussuba



السورة: Suratul Qalam

الآية : 18

وَلَا يَسۡتَثۡنُونَ

Ba sa kuma togaciya (da faxar insha Allah)



السورة: Suratul Qalam

الآية : 19

فَطَافَ عَلَيۡهَا طَآئِفٞ مِّن رَّبِّكَ وَهُمۡ نَآئِمُونَ

Sai wani bala’i daga Ubangijinka ya kewaye ta alhali su suna bacci



السورة: Suratul Qalam

الآية : 20

فَأَصۡبَحَتۡ كَٱلصَّرِيمِ

Sai ta wayi gari (baqi qirin) kamar duhun dare



السورة: Suratul Qalam

الآية : 21

فَتَنَادَوۡاْ مُصۡبِحِينَ

Sai suka kirawo junansu da asussuba



السورة: Suratul Qalam

الآية : 22

أَنِ ٱغۡدُواْ عَلَىٰ حَرۡثِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰرِمِينَ

Cewa: “Ku yi sammako ga amfanin gonarku idan kun kasance masu yin girbi.”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 23

فَٱنطَلَقُواْ وَهُمۡ يَتَخَٰفَتُونَ

Sai suka tafi alhali suna yi wa junansu raxa



السورة: Suratul Qalam

الآية : 24

أَن لَّا يَدۡخُلَنَّهَا ٱلۡيَوۡمَ عَلَيۡكُم مِّسۡكِينٞ

Cewa: “Lalle a yau kada wani miskini ya shigar muku cikinta.”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 25

وَغَدَوۡاْ عَلَىٰ حَرۡدٖ قَٰدِرِينَ

Suka kuwa yi sammako suna masu zaton su masu iko ne a kan hana (mabuqata)



السورة: Suratul Qalam

الآية : 26

فَلَمَّا رَأَوۡهَا قَالُوٓاْ إِنَّا لَضَآلُّونَ

To lokacin da suka gan ta sai suka ce: “Lalle mu tabbas mun yi vatan kai