السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 49

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ لَعَلَّهُمۡ يَهۡتَدُونَ

Haqiqa kuma Mun bai wa Musa Littafi (wato Attaura) don su shiriya



السورة: Suratul Furqan

الآية : 35

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ وَجَعَلۡنَا مَعَهُۥٓ أَخَاهُ هَٰرُونَ وَزِيرٗا

Haqiqa kuma Mun bai wa Musa Littafi muka kuma sanya xan’uwansa Haruna tare da shi a matsayin Waziri



السورة: Suratul Qasas

الآية : 48

فَلَمَّا جَآءَهُمُ ٱلۡحَقُّ مِنۡ عِندِنَا قَالُواْ لَوۡلَآ أُوتِيَ مِثۡلَ مَآ أُوتِيَ مُوسَىٰٓۚ أَوَلَمۡ يَكۡفُرُواْ بِمَآ أُوتِيَ مُوسَىٰ مِن قَبۡلُۖ قَالُواْ سِحۡرَانِ تَظَٰهَرَا وَقَالُوٓاْ إِنَّا بِكُلّٖ كَٰفِرُونَ

To lokacin da gaskiya ta zo musu daga wajenmu sai suka ce: “Ina ma da an ba shi irin abin da aka bai wa Musa?” Yanzu ashe tun da can ba su kafirce da abin da aka bai wa Musa ba; suka ce: “Su biyun sihiri ne (wato Alqur’ani da Attaura) da suke taimakon juna?” Suka kuma ce: “Lalle mu mun kafirce da su gaba xaya.”



السورة: Suratul Qasas

الآية : 49

قُلۡ فَأۡتُواْ بِكِتَٰبٖ مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِ هُوَ أَهۡدَىٰ مِنۡهُمَآ أَتَّبِعۡهُ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Ka ce (da su): “To ku zo da wani littafi daga wajen Allah wanda ya fi su nuna hanyar shiriya (wato Alqur’ani da Attaura), zan bi shi idan kun kasance masu gaskiya.”



السورة: Suratul Qasas

الآية : 50

فَإِن لَّمۡ يَسۡتَجِيبُواْ لَكَ فَٱعۡلَمۡ أَنَّمَا يَتَّبِعُونَ أَهۡوَآءَهُمۡۚ وَمَنۡ أَضَلُّ مِمَّنِ ٱتَّبَعَ هَوَىٰهُ بِغَيۡرِ هُدٗى مِّنَ ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

To idan ba su amsa maka ba, to ka sani cewa ba abin da suke bi sai soye-soyen zukatansu kawai. Ba kuwa wanda ya fi vacewa kamar wanda ya bi son zuciyarsa ba tare da wata shiriya daga Allah ba. Lalle Allah ba Ya shiryar da mutane azzalumai



السورة: Suratus Sajda

الآية : 23

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ فَلَا تَكُن فِي مِرۡيَةٖ مِّن لِّقَآئِهِۦۖ وَجَعَلۡنَٰهُ هُدٗى لِّبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Haqiqa kuma Mu Mun bai wa Musa Littafi, to kada ka kasance (kai Manzo) cikin kokwanto na saduwa da shi (Musan)[1]. Kuma Mun sanya shi ya zamanto shiriya ga Banu-Isra’ila


1- Watau haxuwar Annabi Muhammad () da Annabi Musa () a daren mi’iraji.


السورة: Suratu Ghafir

الآية : 53

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡهُدَىٰ وَأَوۡرَثۡنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱلۡكِتَٰبَ

Kuma haqiqa Mun bai wa Musa shiriya, Muka kuwa gadar wa Banu-Isra’ila littafin (Attaura)



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 54

هُدٗى وَذِكۡرَىٰ لِأُوْلِي ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Don shiriya da wa’azantuwa ga masu hankali



السورة: Suratu Fussilat

الآية : 45

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ فَٱخۡتُلِفَ فِيهِۚ وَلَوۡلَا كَلِمَةٞ سَبَقَتۡ مِن رَّبِّكَ لَقُضِيَ بَيۡنَهُمۡۚ وَإِنَّهُمۡ لَفِي شَكّٖ مِّنۡهُ مُرِيبٖ

Haqiqa Mun bai wa Musa Littafin (Attaura), sai aka yi savani a cikinsa, kuma ba don Kalma ta gabata daga Ubangijinka ba, tabbas da an yi hukunci a tsakaninsu. Lalle kuma su, tabbas suna cikin shakka mai sa kokwanto a game da shi



السورة: Suratun Najm

الآية : 36

أَمۡ لَمۡ يُنَبَّأۡ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىٰ

Ko ba a ba shi labarin abin da yake cikin takardun Musa ba ne?



السورة: Suratun Najm

الآية : 37

وَإِبۡرَٰهِيمَ ٱلَّذِي وَفَّىٰٓ

Da kuma Ibrahimu wanda ya cika alqawari?



السورة: Suratun Najm

الآية : 38

أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٞ وِزۡرَ أُخۡرَىٰ

Cewa: “Wani rai ba ya xaukar nauyin laifin wani



السورة: Suratun Najm

الآية : 39

وَأَن لَّيۡسَ لِلۡإِنسَٰنِ إِلَّا مَا سَعَىٰ

“Kuma mutum bai mallaki wani sakamako ba sai na abin da ya aikata



السورة: Suratun Najm

الآية : 40

وَأَنَّ سَعۡيَهُۥ سَوۡفَ يُرَىٰ

“Kuma lalle aikin nasa ba da daxewa ba za a gan shi



السورة: Suratun Najm

الآية : 41

ثُمَّ يُجۡزَىٰهُ ٱلۡجَزَآءَ ٱلۡأَوۡفَىٰ

“Sannan a saka masa da cikakken sakamako



السورة: Suratun Najm

الآية : 42

وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلۡمُنتَهَىٰ

“Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makoma



السورة: Suratun Najm

الآية : 43

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَضۡحَكَ وَأَبۡكَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ya sa a yi dariya, kuma Ya sa a yi kuka



السورة: Suratun Najm

الآية : 44

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَمَاتَ وَأَحۡيَا

“Kuma lalle Shi ne Ya kashe kuma Ya raya



السورة: Suratun Najm

الآية : 45

وَأَنَّهُۥ خَلَقَ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ya halicci dangi biyu namiji da mace



السورة: Suratun Najm

الآية : 46

مِن نُّطۡفَةٍ إِذَا تُمۡنَىٰ

“Daga maniyyi yayin da ake zuba shi



السورة: Suratun Najm

الآية : 47

وَأَنَّ عَلَيۡهِ ٱلنَّشۡأَةَ ٱلۡأُخۡرَىٰ

“Kuma lalle Ya xora wa kansa sake tashin matattu



السورة: Suratun Najm

الآية : 48

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَغۡنَىٰ وَأَقۡنَىٰ

“Lalle kuma Shi ne Ya wadata, Ya kuma yalwata



السورة: Suratun Najm

الآية : 49

وَأَنَّهُۥ هُوَ رَبُّ ٱلشِّعۡرَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ubangijin tauraron nan Shi’ira



السورة: Suratun Najm

الآية : 50

وَأَنَّهُۥٓ أَهۡلَكَ عَادًا ٱلۡأُولَىٰ

“Lalle kuma Ya hallakar da Adawa na farko



السورة: Suratun Najm

الآية : 51

وَثَمُودَاْ فَمَآ أَبۡقَىٰ

“Da kuma Samudawa, don haka bai bar saura ba



السورة: Suratun Najm

الآية : 52

وَقَوۡمَ نُوحٖ مِّن قَبۡلُۖ إِنَّهُمۡ كَانُواْ هُمۡ أَظۡلَمَ وَأَطۡغَىٰ

“Da mutanen Nuhu tun kafin su; lalle su sun kasance su ne mafiya zalunci kuma mafiya xagawa



السورة: Suratun Najm

الآية : 53

وَٱلۡمُؤۡتَفِكَةَ أَهۡوَىٰ

“Da waxanda aka kife (mutanen Luxu, Allah) ya qasqanta su



السورة: Suratun Najm

الآية : 54

فَغَشَّىٰهَا مَا غَشَّىٰ

“Sannan abin da ya lulluve su (na azaba) ya lulluve su.”



السورة: Suratul Hadid

الآية : 25

لَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا رُسُلَنَا بِٱلۡبَيِّنَٰتِ وَأَنزَلۡنَا مَعَهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمِيزَانَ لِيَقُومَ ٱلنَّاسُ بِٱلۡقِسۡطِۖ وَأَنزَلۡنَا ٱلۡحَدِيدَ فِيهِ بَأۡسٞ شَدِيدٞ وَمَنَٰفِعُ لِلنَّاسِ وَلِيَعۡلَمَ ٱللَّهُ مَن يَنصُرُهُۥ وَرُسُلَهُۥ بِٱلۡغَيۡبِۚ إِنَّ ٱللَّهَ قَوِيٌّ عَزِيزٞ

Haqiqa Mun aiko manzanninmu da (ayoyi) mabayyana, Muka kuma saukar da littafi da ma’auni a tare da su (manzannin) don mutane su tsaya da adalci; Muka kuma saukar da baqin qarfe wanda a tare da shi akwai tsananin qarfi da kuma amfani ga mutane, don kuma Allah Ya bayyanar da wanda yake taimakon Sa da manzanninsa a voye. Lalle Allah Mai qarfi ne, Mabuwayi



السورة: Suratul Hadid

الآية : 26

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا نُوحٗا وَإِبۡرَٰهِيمَ وَجَعَلۡنَا فِي ذُرِّيَّتِهِمَا ٱلنُّبُوَّةَ وَٱلۡكِتَٰبَۖ فَمِنۡهُم مُّهۡتَدٖۖ وَكَثِيرٞ مِّنۡهُمۡ فَٰسِقُونَ

Haqiqa kuma Mun aiko Nuhu da Ibrahimu, Muka kuma sanya annabta da littafi cikin zuriyarsu; To daga cikinsu akwai shiryayyu, masu yawa kuwa daga cikinsu fasiqai ne