السورة: Suratul A’araf

الآية : 73

وَإِلَىٰ ثَمُودَ أَخَاهُمۡ صَٰلِحٗاۚ قَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥۖ قَدۡ جَآءَتۡكُم بَيِّنَةٞ مِّن رَّبِّكُمۡۖ هَٰذِهِۦ نَاقَةُ ٱللَّهِ لَكُمۡ ءَايَةٗۖ فَذَرُوهَا تَأۡكُلۡ فِيٓ أَرۡضِ ٱللَّهِۖ وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٖ فَيَأۡخُذَكُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Zuwa ga Samudawa kuwa Mun aika xan’uwansu Salihu. Ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi; haqiqa hujja ta zo muku daga Ubangijinku. Wannan kuma taguwar Allah aya ce a gare ku; don haka ku qyale ta ta ci a bayan qasar Allah; kuma kar ku tava ta da wani mugun abu, sai wata azaba mai raxaxi ta shafe ku



السورة: Suratul A’araf

الآية : 74

وَٱذۡكُرُوٓاْ إِذۡ جَعَلَكُمۡ خُلَفَآءَ مِنۢ بَعۡدِ عَادٖ وَبَوَّأَكُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ تَتَّخِذُونَ مِن سُهُولِهَا قُصُورٗا وَتَنۡحِتُونَ ٱلۡجِبَالَ بُيُوتٗاۖ فَٱذۡكُرُوٓاْ ءَالَآءَ ٱللَّهِ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

“Kuma ku tuna lokacin da Ya sanya ku kuka zama masu maye gurbi bayan Adawa, kuma Ya zaunar da ku a bayan qasa, kuna yin benaye a wurarenta masu taushi, kuma kuna sassaqa gidaje a duwatsu; don haka ku tuna ni’imomin Allah, kada kuma ku yi varna a bayan qasa.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 75

قَالَ ٱلۡمَلَأُ ٱلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُواْ مِن قَوۡمِهِۦ لِلَّذِينَ ٱسۡتُضۡعِفُواْ لِمَنۡ ءَامَنَ مِنۡهُمۡ أَتَعۡلَمُونَ أَنَّ صَٰلِحٗا مُّرۡسَلٞ مِّن رَّبِّهِۦۚ قَالُوٓاْ إِنَّا بِمَآ أُرۡسِلَ بِهِۦ مُؤۡمِنُونَ

Manyan gari waxanda suka yi girman kai daga mutanensa, suka ce wa waxanda suke raunana waxanda suka yi imani daga cikinsu: “Yanzu kun san cewa Salihu Manzo ne daga wajen Ubangijinsa?” Sai suka ce; “Lalle mu dai mun yi imani da abin da aka aiko shi da shi.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 76

قَالَ ٱلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُوٓاْ إِنَّا بِٱلَّذِيٓ ءَامَنتُم بِهِۦ كَٰفِرُونَ

Waxanda suka yi girman kai suka ce: “Lalle mu kuma mun kafirce wa abin da kuka yi imani da shi.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 77

فَعَقَرُواْ ٱلنَّاقَةَ وَعَتَوۡاْ عَنۡ أَمۡرِ رَبِّهِمۡ وَقَالُواْ يَٰصَٰلِحُ ٱئۡتِنَا بِمَا تَعِدُنَآ إِن كُنتَ مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Sai suka soke taguwar, suka kuma yi tsaurin kai game da umarnin Ubangijinsu, kuma suka ce: “Ya Salihu, ka zo mana da abin da kake mana alqawarin zai same mu (na azaba) in ka kasance cikin manzanni.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 78

فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلرَّجۡفَةُ فَأَصۡبَحُواْ فِي دَارِهِمۡ جَٰثِمِينَ

Sai wata girgizar qasa mai tsanani ta auka musu, sai suka wayi gari a gurfane kan gwiwoyinsu, (matattu) a cikin gidajensu



السورة: Suratul A’araf

الآية : 79

فَتَوَلَّىٰ عَنۡهُمۡ وَقَالَ يَٰقَوۡمِ لَقَدۡ أَبۡلَغۡتُكُمۡ رِسَالَةَ رَبِّي وَنَصَحۡتُ لَكُمۡ وَلَٰكِن لَّا تُحِبُّونَ ٱلنَّـٰصِحِينَ

Sai ya juya ya rabu da su, kuma ya ce: “Ya ku mutanena, lalle haqiqa na isar muku da saqon Ubangijina, kuma na yi muku nasiha, sai dai ku ba kwa son masu nasiha.”



السورة: Suratu Hud

الآية : 61

۞وَإِلَىٰ ثَمُودَ أَخَاهُمۡ صَٰلِحٗاۚ قَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥۖ هُوَ أَنشَأَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ وَٱسۡتَعۡمَرَكُمۡ فِيهَا فَٱسۡتَغۡفِرُوهُ ثُمَّ تُوبُوٓاْ إِلَيۡهِۚ إِنَّ رَبِّي قَرِيبٞ مُّجِيبٞ

Haka kuma Muka aiko wa Samudawa xan’uwansu Salihu. Ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta ba shi ba; Shi ne Ya halicce ku daga qasa, Ya kuma ba ku damar ku raya ta; to ku nemi gafararsa sannan ku tuba gare Shi. Lalle Ubangijina Makusanci ne, Mai amsawa.”



السورة: Suratu Hud

الآية : 62

قَالُواْ يَٰصَٰلِحُ قَدۡ كُنتَ فِينَا مَرۡجُوّٗا قَبۡلَ هَٰذَآۖ أَتَنۡهَىٰنَآ أَن نَّعۡبُدَ مَا يَعۡبُدُ ءَابَآؤُنَا وَإِنَّنَا لَفِي شَكّٖ مِّمَّا تَدۡعُونَآ إِلَيۡهِ مُرِيبٖ

Suka ce: “Ya Salihu, haqiqa a da ka kasance a cikinmu abin yi wa (kyakkyawan) fata kafin (ka zo mana da) wannan; yanzu ka riqa hana mu mu bauta wa abin da iyayenmu suke bauta wa? Lalle mu kam tabbas muna matuqar shakka game da abin da kake kiran mu gare shi.”



السورة: Suratu Hud

الآية : 63

قَالَ يَٰقَوۡمِ أَرَءَيۡتُمۡ إِن كُنتُ عَلَىٰ بَيِّنَةٖ مِّن رَّبِّي وَءَاتَىٰنِي مِنۡهُ رَحۡمَةٗ فَمَن يَنصُرُنِي مِنَ ٱللَّهِ إِنۡ عَصَيۡتُهُۥۖ فَمَا تَزِيدُونَنِي غَيۡرَ تَخۡسِيرٖ

Ya ce: “Ya ku mutanena, ku ba ni labari, yanzu idan na kasance a kan bayyananniyar hujja daga Ubangijina, Ya kuma ba ni rahama (ta annabci) to wa zai kare ni daga (azabar) Allah idan na sava masa? Don haka babu abin da za ku qare ni da shi in ban da tavewa.”



السورة: Suratu Hud

الآية : 64

وَيَٰقَوۡمِ هَٰذِهِۦ نَاقَةُ ٱللَّهِ لَكُمۡ ءَايَةٗۖ فَذَرُوهَا تَأۡكُلۡ فِيٓ أَرۡضِ ٱللَّهِۖ وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٖ فَيَأۡخُذَكُمۡ عَذَابٞ قَرِيبٞ

“Kuma ya ku mutanena, wannan fa taguwar Allah ce a gare ku, sai ku bar ta ta ci a qasar Allah, kada ku cutar da ita, sai azaba ta kusa-kusa ta afka muku.”



السورة: Suratu Hud

الآية : 65

فَعَقَرُوهَا فَقَالَ تَمَتَّعُواْ فِي دَارِكُمۡ ثَلَٰثَةَ أَيَّامٖۖ ذَٰلِكَ وَعۡدٌ غَيۡرُ مَكۡذُوبٖ

Amma sai suka soke ta, sai ya ce (da su): “Ku ji daxi cikin gidajenku kwana uku (rak). Wannan alqawari ne ba abin qaryatawa ba.”



السورة: Suratu Hud

الآية : 66

فَلَمَّا جَآءَ أَمۡرُنَا نَجَّيۡنَا صَٰلِحٗا وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ بِرَحۡمَةٖ مِّنَّا وَمِنۡ خِزۡيِ يَوۡمِئِذٍۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ ٱلۡقَوِيُّ ٱلۡعَزِيزُ

To lokacin da umarninmu ya zo sai Muka tserar da Salihu shi da waxanda suka yi imani tare da shi saboda wata rahama daga gare mu, kuma (Muka tserar da su) daga kunyatar wannan rana. Lalle Ubangijinka Shi ne Mai qarfi Mabuwayi



السورة: Suratu Hud

الآية : 67

وَأَخَذَ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ ٱلصَّيۡحَةُ فَأَصۡبَحُواْ فِي دِيَٰرِهِمۡ جَٰثِمِينَ

Kuma tsawa ta kama waxanda suka yi zalunci, sai suka wayi gari cikin gidajensu a duddurqushe (babu rai)



السورة: Suratu Hud

الآية : 68

كَأَن لَّمۡ يَغۡنَوۡاْ فِيهَآۗ أَلَآ إِنَّ ثَمُودَاْ كَفَرُواْ رَبَّهُمۡۗ أَلَا بُعۡدٗا لِّثَمُودَ

Kamar daxai ba su tava zama a cikinsu ba (gidajen). Ku saurara! Lalle Samudawa kam sun kafirce wa Ubangijinsu. Ku saurara! Halaka ta tabbata ga Samudawa



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 141

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Samudawa sun qaryata manzanni[1]


1- Domin qaryata Annabi Salihu () daidai yake da qaryata duk manzannin Allah, saboda saqo iri xaya suke xauke da shi.


السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 142

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ صَٰلِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da xan’uwansu Salihu ya ce da su: “Yanzu ba kwa yi taqawa ba?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 143

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce gare ku



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 144

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 145

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 146

أَتُتۡرَكُونَ فِي مَا هَٰهُنَآ ءَامِنِينَ

“Yanzu (zatonku) za a bar ku ne cikin abin da yake a nan (duniya) cikin kwanciyar hankali?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 147

فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

“(Watau) a cikin gonaki da idandunan ruwa?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 148

وَزُرُوعٖ وَنَخۡلٖ طَلۡعُهَا هَضِيمٞ

“Da shuke-shuke da dabinai masu taushin ‘ya’ya?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 149

وَتَنۡحِتُونَ مِنَ ٱلۡجِبَالِ بُيُوتٗا فَٰرِهِينَ

“Kuma kuna fafe duwatsu kuna yin gidaje kuna masu nuna qwarewa?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 150

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 151

وَلَا تُطِيعُوٓاْ أَمۡرَ ٱلۡمُسۡرِفِينَ

“Kada kuma ku bi umarnin mavarnata



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 152

ٱلَّذِينَ يُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا يُصۡلِحُونَ

“Waxanda suke varna a bayan qasa, kuma ba sa gyara.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 153

قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ

Suka ce: “Lalle kai kana daga waxanda aka sihirce ne kawai



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 154

مَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا فَأۡتِ بِـَٔايَةٍ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

“Kai ba kowa ba ne sai mutum kamarmu, to ka zo mana da aya idan ka kasance daga masu gaskiya.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 155

قَالَ هَٰذِهِۦ نَاقَةٞ لَّهَا شِرۡبٞ وَلَكُمۡ شِرۡبُ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ

(Salihu) ya ce: “Wannan taguwa ce[1], tana da (ranar) shanta ku ma kuna da rana sananniya ta shanku


1- Watau a matsayin mu’ujiza ga Annabi Salihu ().