السورة: Suratur Ra’ad

الآية : 1

الٓمٓرۚ تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِۗ وَٱلَّذِيٓ أُنزِلَ إِلَيۡكَ مِن رَّبِّكَ ٱلۡحَقُّ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يُؤۡمِنُونَ

ALIF LAM MIM RA[1]. Waxannan ayoyi ne na Littafi (wato Alqur’ani). Wanda kuma aka saukar maka daga Ubangijinka gaskiya ne, sai dai lalle yawancin mutane ba sa yin imani


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


السورة: Suratur Ra’ad

الآية : 36

وَٱلَّذِينَ ءَاتَيۡنَٰهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ يَفۡرَحُونَ بِمَآ أُنزِلَ إِلَيۡكَۖ وَمِنَ ٱلۡأَحۡزَابِ مَن يُنكِرُ بَعۡضَهُۥۚ قُلۡ إِنَّمَآ أُمِرۡتُ أَنۡ أَعۡبُدَ ٱللَّهَ وَلَآ أُشۡرِكَ بِهِۦٓۚ إِلَيۡهِ أَدۡعُواْ وَإِلَيۡهِ مَـَٔابِ

Waxanda kuwa Muka bai wa littafi (muminansu) suna farin ciki da abin da aka saukar maka; akwai kuma wasu daga qungiyoyi waxanda suke musun wani sashi nasa. Ka ce: “Ni dai an umarce ni ne kawai da in bauta wa Allah, kada kuma in tara wani abu da Shi. Kuma zuwa gare Shi kawai nake kira, wurinsa ne kawai kuma makomata.”



السورة: Suratu Ibrahim

الآية : 1

الٓرۚ كِتَٰبٌ أَنزَلۡنَٰهُ إِلَيۡكَ لِتُخۡرِجَ ٱلنَّاسَ مِنَ ٱلظُّلُمَٰتِ إِلَى ٱلنُّورِ بِإِذۡنِ رَبِّهِمۡ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

ALIF LAM RA[1]. Littafi ne da Muka saukar maka da shi, don ka fitar da mutane daga duffai zuwa ga haske, da izinin Ubangijinsu zuwa ga tafarkin (Allah) Mabuwayi, Abin godiya


1- Duba Suratul Baqara aya ta 1, hashiya ta 8.


السورة: Suratul Hijr

الآية : 9

إِنَّا نَحۡنُ نَزَّلۡنَا ٱلذِّكۡرَ وَإِنَّا لَهُۥ لَحَٰفِظُونَ

Lalle Mu Muka saukar da Alqur’ani, lalle kuma tabbas Mu za Mu kiyaye shi



السورة: Suratul Hijr

الآية : 87

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَٰكَ سَبۡعٗا مِّنَ ٱلۡمَثَانِي وَٱلۡقُرۡءَانَ ٱلۡعَظِيمَ

Haqiqa kuma Mun ba ka (ayoyi) bakwai waxanda ake ta nanatawa (wato Suratul Fatiha) da kuma Alqur’ani mai girma



السورة: Suratun Nahl

الآية : 24

وَإِذَا قِيلَ لَهُم مَّاذَآ أَنزَلَ رَبُّكُمۡ قَالُوٓاْ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Idan kuma aka ce da su: “Me Ubangijinku Ya saukar?” (Sai) su ce: “Tatsuniyoyin mutanen farko.”



السورة: Suratun Nahl

الآية : 44

بِٱلۡبَيِّنَٰتِ وَٱلزُّبُرِۗ وَأَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلذِّكۡرَ لِتُبَيِّنَ لِلنَّاسِ مَا نُزِّلَ إِلَيۡهِمۡ وَلَعَلَّهُمۡ يَتَفَكَّرُونَ

(Mun aiko su) da hujjoji bayyanannu da littattafai. Mun kuma saukar maka da Alqur’ani don ka yi wa mutane bayanin abin da aka saukar musu ko sa yi tunani



السورة: Suratun Nahl

الآية : 64

وَمَآ أَنزَلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ إِلَّا لِتُبَيِّنَ لَهُمُ ٱلَّذِي ٱخۡتَلَفُواْ فِيهِ وَهُدٗى وَرَحۡمَةٗ لِّقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ

Kuma ba Mu saukar maka da Littafi ba sai don ka yi musu bayanin abin da suka yi savani game da shi, kuma shiriya ne da rahama ga mutanen da suke yin imani



السورة: Suratun Nahl

الآية : 89

وَيَوۡمَ نَبۡعَثُ فِي كُلِّ أُمَّةٖ شَهِيدًا عَلَيۡهِم مِّنۡ أَنفُسِهِمۡۖ وَجِئۡنَا بِكَ شَهِيدًا عَلَىٰ هَـٰٓؤُلَآءِۚ وَنَزَّلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ تِبۡيَٰنٗا لِّكُلِّ شَيۡءٖ وَهُدٗى وَرَحۡمَةٗ وَبُشۡرَىٰ لِلۡمُسۡلِمِينَ

Kuma (ka tuna) ranar da za Mu tayar wa kowace al’umma da mai ba da shaida a kansu daga jinsinsu, Mu kuma zo da kai (Annabi Muhammadu) shaida a kan waxannan (wato al’ummarka). Kuma Mun saukar maka da Littafi ne (wato Alqur’ani) don bayani ga kowanne abu, kuma shiriya da rahama da bushara ga Musulmi



السورة: Suratun Nahl

الآية : 98

فَإِذَا قَرَأۡتَ ٱلۡقُرۡءَانَ فَٱسۡتَعِذۡ بِٱللَّهِ مِنَ ٱلشَّيۡطَٰنِ ٱلرَّجِيمِ

To idan za ka karanta Alqur’ani sai ka nemi tsarin Allah daga Shaixan korarre (daga rahamar Allah)



السورة: Suratun Nahl

الآية : 101

وَإِذَا بَدَّلۡنَآ ءَايَةٗ مَّكَانَ ءَايَةٖ وَٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا يُنَزِّلُ قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مُفۡتَرِۭۚ بَلۡ أَكۡثَرُهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Idan kuma Muka musanya wata aya a madadin wata ayar, alhali kuwa Allah ne Mafi sanin abin da Yake saukarwa, sai su ce: “Kai dai mai qirqirar qarya ne kawai!” A’a, ba haka ba ne, yawancinsu ba su san (komai) ba ne



السورة: Suratun Nahl

الآية : 102

قُلۡ نَزَّلَهُۥ رُوحُ ٱلۡقُدُسِ مِن رَّبِّكَ بِٱلۡحَقِّ لِيُثَبِّتَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَهُدٗى وَبُشۡرَىٰ لِلۡمُسۡلِمِينَ

Ka ce: “Ruhul Qudusi (watau Mala’ika Jibrilu) ne ya saukar da shi daga Ubangijinka da gaskiya don ya tabbatar da waxanda suka yi imani (a kan dugadugansu), kuma shiriya ne da albishir ga Musulmai.”



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 9

إِنَّ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانَ يَهۡدِي لِلَّتِي هِيَ أَقۡوَمُ وَيُبَشِّرُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ ٱلَّذِينَ يَعۡمَلُونَ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أَنَّ لَهُمۡ أَجۡرٗا كَبِيرٗا

Lalle wannan Alqur’anin yana shiryarwa ne ga (hanya) mafi miqewa, yana kuma yi wa muminai waxanda suke yin kyawawan ayyuka albishir cewa, lalle suna da lada mai girma



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 46

وَجَعَلۡنَا عَلَىٰ قُلُوبِهِمۡ أَكِنَّةً أَن يَفۡقَهُوهُ وَفِيٓ ءَاذَانِهِمۡ وَقۡرٗاۚ وَإِذَا ذَكَرۡتَ رَبَّكَ فِي ٱلۡقُرۡءَانِ وَحۡدَهُۥ وَلَّوۡاْ عَلَىٰٓ أَدۡبَٰرِهِمۡ نُفُورٗا

Kuma Mukan sanya marufi a kan zukatansu don kada su fahimce shi (Alqur’anin); a cikin kunnuwansu kuma (Mukan sanya) wani nauyi. Idan kuma ka ambaci Ubangijinka Shi kaxai a cikin Alqur’ani sai su ba da baya suna masu bazama



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 88

قُل لَّئِنِ ٱجۡتَمَعَتِ ٱلۡإِنسُ وَٱلۡجِنُّ عَلَىٰٓ أَن يَأۡتُواْ بِمِثۡلِ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانِ لَا يَأۡتُونَ بِمِثۡلِهِۦ وَلَوۡ كَانَ بَعۡضُهُمۡ لِبَعۡضٖ ظَهِيرٗا

Ka ce da su: “Lalle da mutane da aljannu sun haxu kan su kawo irin wannan Alqur’anin, to ba za su zo da irinsa ba, ko da kuwa wasu sun zamanto suna taimaka wa wasu.”



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 105

وَبِٱلۡحَقِّ أَنزَلۡنَٰهُ وَبِٱلۡحَقِّ نَزَلَۗ وَمَآ أَرۡسَلۡنَٰكَ إِلَّا مُبَشِّرٗا وَنَذِيرٗا

Kuma da gaskiya Muka saukar da shi (Alqur’ani), kuma da gaskiya ya sauko. Ba Mu kuma aiko ka ba sai mai yin albishir, mai kuma gargaxi



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 106

وَقُرۡءَانٗا فَرَقۡنَٰهُ لِتَقۡرَأَهُۥ عَلَى ٱلنَّاسِ عَلَىٰ مُكۡثٖ وَنَزَّلۡنَٰهُ تَنزِيلٗا

Kuma Mun saukar da Qur’ani, Mun bayyana shi don ka karanta wa mutane shi a sannu a hankali, Mun kuma saukar da shi daki-daki



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 107

قُلۡ ءَامِنُواْ بِهِۦٓ أَوۡ لَا تُؤۡمِنُوٓاْۚ إِنَّ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡعِلۡمَ مِن قَبۡلِهِۦٓ إِذَا يُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ يَخِرُّونَۤ لِلۡأَذۡقَانِۤ سُجَّدٗاۤ

Ka ce da su: “Ko ku yi imani da shi ko kada ku yi imani da shi (duk xaya ne).” Lalle waxanda aka bai wa ilimi gabaninsa (Yahudu da Nasara)[1] idan ana karanta musu shi suna faxuwa da fuskokinsu suna masu sujjada


1- Watau mutanen kirki daga cikinsu.


السورة: Suratul Kahf 

الآية : 1

ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِيٓ أَنزَلَ عَلَىٰ عَبۡدِهِ ٱلۡكِتَٰبَ وَلَمۡ يَجۡعَل لَّهُۥ عِوَجَاۜ

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah wanda Ya saukar wa da Bawansa Littafi, bai kuma sanya masa wata karkata ba



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 2

قَيِّمٗا لِّيُنذِرَ بَأۡسٗا شَدِيدٗا مِّن لَّدُنۡهُ وَيُبَشِّرَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ ٱلَّذِينَ يَعۡمَلُونَ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أَنَّ لَهُمۡ أَجۡرًا حَسَنٗا

Daidaitacce ne, don ya yi gargaxi game da azaba mai tsanani daga gare Shi (wato Allah), ya kuma yi wa muminai waxanda suke aiki nagari albishir cewa suna da lada kyakkyawa



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 27

وَٱتۡلُ مَآ أُوحِيَ إِلَيۡكَ مِن كِتَابِ رَبِّكَۖ لَا مُبَدِّلَ لِكَلِمَٰتِهِۦ وَلَن تَجِدَ مِن دُونِهِۦ مُلۡتَحَدٗا

Kuma ka karanta abin da aka yiwo maka wahayi da shi daga littafin Ubangijinka: Ba mai canja kalmominsa; ba kuma za ka sami wata mafaka ba in ba ta wurinsa ba



السورة: Suratu Maryam

الآية : 58

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ أَنۡعَمَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِم مِّنَ ٱلنَّبِيِّـۧنَ مِن ذُرِّيَّةِ ءَادَمَ وَمِمَّنۡ حَمَلۡنَا مَعَ نُوحٖ وَمِن ذُرِّيَّةِ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡرَـٰٓءِيلَ وَمِمَّنۡ هَدَيۡنَا وَٱجۡتَبَيۡنَآۚ إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُ ٱلرَّحۡمَٰنِ خَرُّواْۤ سُجَّدٗاۤ وَبُكِيّٗا۩

Waxannan su ne annabawa waxanda Allah Ya yi ni’ima a gare su, daga zuriyar Adamu, da kuma waxanda Muka xauko (a jirgin ruwa) tare da Nuhu, daga kuma zuriyar Ibrahimu da Isra’ila (watau Ya’aqubu), da kuma waxanda Muka shiryar da su Muka kuma zave su. Idan ana karanta musu ayoyin (Allah) Mai rahama sai su faxi su yi sujjada suna kuka



السورة: Suratu Maryam

الآية : 73

وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ قَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لِلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَيُّ ٱلۡفَرِيقَيۡنِ خَيۡرٞ مَّقَامٗا وَأَحۡسَنُ نَدِيّٗا

Kuma idan ana karanta musu ayoyinmu bayyanannu sai waxanda suka kafirta su ce da waxanda suka yi imani: “Wane ne daga cikin qungiyoyin nan biyu (watau muminai da kafirai) yake da mafificin matsayi da kuma mafi kyan majalisa?”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 10

لَقَدۡ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكُمۡ كِتَٰبٗا فِيهِ ذِكۡرُكُمۡۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Haqiqa Mun saukar muku da littafi (wanda) a cikinsa akwai xaukakarku[1]; me ya sa ba kwa hankalta?


1- Watau za su samu xaukaka duniya da lahira idan sun yi imani da shi, suka yi aiki da karantarwarsa.


السورة: Suratul Anbiya

الآية : 50

وَهَٰذَا ذِكۡرٞ مُّبَارَكٌ أَنزَلۡنَٰهُۚ أَفَأَنتُمۡ لَهُۥ مُنكِرُونَ

Wannan (Alqur’ani) kuwa tunatarwa ne mai albarka da Muka saukar da shi. Shin ku yanzu kwa riqa musun sa?



السورة: Suratul Hajji

الآية : 16

وَكَذَٰلِكَ أَنزَلۡنَٰهُ ءَايَٰتِۭ بَيِّنَٰتٖ وَأَنَّ ٱللَّهَ يَهۡدِي مَن يُرِيدُ

Kamar haka kuwa Muka saukar da shi (Alqur’ani) ayoyi mabayyana, kuma lalle Allah Yana shiryar da wanda Yake nufin (shiryar da shi)



السورة: Suratul Hajji

الآية : 54

وَلِيَعۡلَمَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡعِلۡمَ أَنَّهُ ٱلۡحَقُّ مِن رَّبِّكَ فَيُؤۡمِنُواْ بِهِۦ فَتُخۡبِتَ لَهُۥ قُلُوبُهُمۡۗ وَإِنَّ ٱللَّهَ لَهَادِ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Don kuma waxanda aka bai wa ilimi su san cewa shi (Alqur’ani) gaskiya ne daga Ubangijinka yake, sai su yi imani da shi sai zukatansu su nutsu da shi. Kuma lalle Allah tabbas Mai shiryar da waxanda suka yi imani ne zuwa ga tafarki madaidaici



السورة: Suratul Hajji

الآية : 72

وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ تَعۡرِفُ فِي وُجُوهِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱلۡمُنكَرَۖ يَكَادُونَ يَسۡطُونَ بِٱلَّذِينَ يَتۡلُونَ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتِنَاۗ قُلۡ أَفَأُنَبِّئُكُم بِشَرّٖ مِّن ذَٰلِكُمُۚ ٱلنَّارُ وَعَدَهَا ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Idan kuma ana karanta musu ayoyinmu bayyanannu, to za ka ga alamar musantawa a fuskokin waxanda suka kafirta, suna kamar za su auka wa waxanda suke karanta musu ayoyinmu. To ka ce: “Shin ba na ba ku labarin abin da ya fi wannan muni ba[1]? Wuta ce da Allah Ya yi alqawari ga waxanda suka kafirta; makoma kuwa ta munana.”


1- Watau fiye da abin da suke ganin muninsa idan ana karanta musu shi, watau ayoyin Alqur’ani.


السورة: Suratun Nur

الآية : 34

وَلَقَدۡ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكُمۡ ءَايَٰتٖ مُّبَيِّنَٰتٖ وَمَثَلٗا مِّنَ ٱلَّذِينَ خَلَوۡاْ مِن قَبۡلِكُمۡ وَمَوۡعِظَةٗ لِّلۡمُتَّقِينَ

Haqiqa kuma Mun saukar muku da ayoyi mabayyana da kuma izina daga waxanda suka wuce gabaninku, kuma da gargaxi ga masu taqawa



السورة: Suratun Nur

الآية : 46

لَّقَدۡ أَنزَلۡنَآ ءَايَٰتٖ مُّبَيِّنَٰتٖۚ وَٱللَّهُ يَهۡدِي مَن يَشَآءُ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Haqiqa Mun saukar da ayoyi masu bayyana komai da komai. Allah kuma Yana shiryar da wanda Ya ga dama zuwa ga tafarki madaidaici