مَٰلِكِ يَوۡمِ ٱلدِّينِ
Mamallakin ranar sakamako
كُلُّ نَفۡسٖ ذَآئِقَةُ ٱلۡمَوۡتِۗ وَإِنَّمَا تُوَفَّوۡنَ أُجُورَكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۖ فَمَن زُحۡزِحَ عَنِ ٱلنَّارِ وَأُدۡخِلَ ٱلۡجَنَّةَ فَقَدۡ فَازَۗ وَمَا ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَآ إِلَّا مَتَٰعُ ٱلۡغُرُورِ
Kowane rai zai xanxani mutuwa. Kuma a ranar alqiyama ne za a cika muku ladan ayyukanku; to duk wanda aka nisanta shi daga wuta, kuma aka shigar da shi Aljanna, to haqiqa ya rabauta. Kuma rayuwar duniya ba komai ba ce face jin daxi mai ruxarwa
وَٱلَّذِيٓ أَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لِي خَطِيٓـَٔتِي يَوۡمَ ٱلدِّينِ
“Wanda kuma nake kwaxayin Ya gafarta min kurakuraina ranar sakamako
وَقَالُواْ يَٰوَيۡلَنَا هَٰذَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Sai su ce: “Kaitonmu!” (Sai a ce da su): “Wannan ita ce ranar sakamako
هَٰذَا يَوۡمُ ٱلۡفَصۡلِ ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
“Wannan ita ce ranar hukunci wadda kuka kasance kuna qaryatawa.”
يَسۡـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Suna tambayar yaushe ne ranar sakamako?
يَوۡمَ هُمۡ عَلَى ٱلنَّارِ يُفۡتَنُونَ
A ranar da su za a azabtar da su kan wuta
ذُوقُواْ فِتۡنَتَكُمۡ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَسۡتَعۡجِلُونَ
(A ce da su): “Ku xanxani azabarku, wannan shi ne abin da kuka kasance kuna neman gaggautowarsa.”
وَإِنَّ ٱلۡفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٖ
Lalle kuma fajirai tabbas suna cikin (wutar) Jahima
يَصۡلَوۡنَهَا يَوۡمَ ٱلدِّينِ
Za su qonu da ita ranar sakamako
وَمَا هُمۡ عَنۡهَا بِغَآئِبِينَ
Kuma su ba masu rabuwa ne da ita ba
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Kuma kai me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?
ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Sannan me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?
يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ
(Ita ce) ranar da wani rai ba ya mallakar wani amfani ga wani rai; al’amari kuwa (gaba xayansa) a wannan ranar yana ga Allah