السورة: Suratul Baqara

الآية : 21

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱعۡبُدُواْ رَبَّكُمُ ٱلَّذِي خَلَقَكُمۡ وَٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تَتَّقُونَ

Ya ku mutane, ku bauta wa Ubangijinku Wanda Ya halicce ku, da waxanda suka gabace ku, don ku samu taqawa



السورة: Suratul Baqara

الآية : 168

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ كُلُواْ مِمَّا فِي ٱلۡأَرۡضِ حَلَٰلٗا طَيِّبٗا وَلَا تَتَّبِعُواْ خُطُوَٰتِ ٱلشَّيۡطَٰنِۚ إِنَّهُۥ لَكُمۡ عَدُوّٞ مُّبِينٌ

Ya ku mutane, ku ci halal mai daxi na abin da ke bayan qasa, kada kuma ku bi hanyoyin Shaixan, lalle shi maqiyi ne mai bayyana qiyayya a gare ku



السورة: Suratul Baqara

الآية : 281

وَٱتَّقُواْ يَوۡمٗا تُرۡجَعُونَ فِيهِ إِلَى ٱللَّهِۖ ثُمَّ تُوَفَّىٰ كُلُّ نَفۡسٖ مَّا كَسَبَتۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Kuma ku kiyayi wani yini da za a mayar da ku zuwa ga Allah a cikinsa, sannan kowane rai za a cika masa abin da ya aiwatar na aiki, kuma su ba za a zalunce su ba



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱتَّقُواْ رَبَّكُمُ ٱلَّذِي خَلَقَكُم مِّن نَّفۡسٖ وَٰحِدَةٖ وَخَلَقَ مِنۡهَا زَوۡجَهَا وَبَثَّ مِنۡهُمَا رِجَالٗا كَثِيرٗا وَنِسَآءٗۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ ٱلَّذِي تَسَآءَلُونَ بِهِۦ وَٱلۡأَرۡحَامَۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلَيۡكُمۡ رَقِيبٗا

Ya ku mutane, ku kiyaye dokokin Ubangijinku Wanda Ya halicce ku daga rai guda xaya, kuma Ya halicci matarsa daga shi, kuma Ya yaxa maza da mata masu yawa daga gare su. Kuma ku kiyaye dokokin Allah Wanda kuke yi wa juna magiya da Shi, kuma ku kiyaye (yanke) zumunci. Lalle Allah Mai kula da ku ne



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 58

۞إِنَّ ٱللَّهَ يَأۡمُرُكُمۡ أَن تُؤَدُّواْ ٱلۡأَمَٰنَٰتِ إِلَىٰٓ أَهۡلِهَا وَإِذَا حَكَمۡتُم بَيۡنَ ٱلنَّاسِ أَن تَحۡكُمُواْ بِٱلۡعَدۡلِۚ إِنَّ ٱللَّهَ نِعِمَّا يَعِظُكُم بِهِۦٓۗ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ سَمِيعَۢا بَصِيرٗا

Lalle Allah Yana umartar ku da ku mayar da amanoni ga masu su, kuma idan za ku yi hukunci a tsakanin mutane, to ku yi hukunci da adalci. Lalle kam madalla da abin da Allah Yake muku wa’azi da shi. Lalle Allah Ya kasance Mai ji ne, Mai gani



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 170

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ قَدۡ جَآءَكُمُ ٱلرَّسُولُ بِٱلۡحَقِّ مِن رَّبِّكُمۡ فَـَٔامِنُواْ خَيۡرٗا لَّكُمۡۚ وَإِن تَكۡفُرُواْ فَإِنَّ لِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Ya ku mutane, haqiqa Manzo ya zo muku da gaskiya daga wajen Ubangijinku, don haka ku yi imani shi ya fi alheri a gare ku. Idan kuwa kuka kafirce, to lalle abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa duk na Allah ne. kuma Allah Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai hikima



السورة: Suratu Ibrahim

الآية : 52

هَٰذَا بَلَٰغٞ لِّلنَّاسِ وَلِيُنذَرُواْ بِهِۦ وَلِيَعۡلَمُوٓاْ أَنَّمَا هُوَ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞ وَلِيَذَّكَّرَ أُوْلُواْ ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Wannan (Alqur’ani) saqo ne ga mutane don kuma a gargaxe su da shi, kuma su san cewa Shi Allah Xaya ne, don kuma ma’abota hankali su wa’azantu



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 89

وَلَقَدۡ صَرَّفۡنَا لِلنَّاسِ فِي هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانِ مِن كُلِّ مَثَلٖ فَأَبَىٰٓ أَكۡثَرُ ٱلنَّاسِ إِلَّا كُفُورٗا

Kuma haqiqa Mun sarrafa wa mutane kowanne irin misali a cikin wannan Alqur’ani, sai dai yawancin mutane sun qi (komai) sai kafircewa



السورة: Suratul Hajji

الآية : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱتَّقُواْ رَبَّكُمۡۚ إِنَّ زَلۡزَلَةَ ٱلسَّاعَةِ شَيۡءٌ عَظِيمٞ

Ya ku mutane, ku kiyaye dokokin Ubangijinku. Lalle girgizar (ranar) alqiyama abu ne mai girma



السورة: Suratu Luqman

الآية : 33

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱتَّقُواْ رَبَّكُمۡ وَٱخۡشَوۡاْ يَوۡمٗا لَّا يَجۡزِي وَالِدٌ عَن وَلَدِهِۦ وَلَا مَوۡلُودٌ هُوَ جَازٍ عَن وَالِدِهِۦ شَيۡـًٔاۚ إِنَّ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٞۖ فَلَا تَغُرَّنَّكُمُ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَا وَلَا يَغُرَّنَّكُم بِٱللَّهِ ٱلۡغَرُورُ

Ya ku mutane, ku kiyaye dokokin Ubangijinku, kuma ku ji tsoron ranar da mahaifi ba zai amfana wa xansa komai ba, kuma xan shi ma ba zai amfana wa mahaifinsa komai ba. Lalle alqawarin Allah gaskiya ne; to kada rayuwar duniya ta ruxe ku, kuma (Shaixan) mai ruxarwa kada ya ruxe ku game da Allah



السورة: Suratu Faxir

الآية : 3

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتَ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡۚ هَلۡ مِنۡ خَٰلِقٍ غَيۡرُ ٱللَّهِ يَرۡزُقُكُم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِۚ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ فَأَنَّىٰ تُؤۡفَكُونَ

Ya ku mutane, ku tuna ni’imar Allah a gare ku. Yanzu akwai wani mahalicci ban da Allah wanda zai arzuta ku daga sama da qasa? Babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. To ta yaya ake karkatar da ku?



السورة: Suratu Faxir

الآية : 5

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ إِنَّ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٞۖ فَلَا تَغُرَّنَّكُمُ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَا وَلَا يَغُرَّنَّكُم بِٱللَّهِ ٱلۡغَرُورُ

Ya ku mutane, lalle alqawarin Allah gaskiya ne, saboda haka kada rayuwar duniya ta ruxe ku; kada kuma mai ruxarwa (Shaixan) ya ruxe ku game da Allah



السورة: Suratu Faxir

الآية : 6

إِنَّ ٱلشَّيۡطَٰنَ لَكُمۡ عَدُوّٞ فَٱتَّخِذُوهُ عَدُوًّاۚ إِنَّمَا يَدۡعُواْ حِزۡبَهُۥ لِيَكُونُواْ مِنۡ أَصۡحَٰبِ ٱلسَّعِيرِ

Lalle Shaixan maqiyinku ne, saboda haka sai ku riqe shi maqiyi. Lalle yana kiran mutanensa ne don su zama ‘yan wuta