السورة: Suratul Mujadila

الآية : 6

يَوۡمَ يَبۡعَثُهُمُ ٱللَّهُ جَمِيعٗا فَيُنَبِّئُهُم بِمَا عَمِلُوٓاْۚ أَحۡصَىٰهُ ٱللَّهُ وَنَسُوهُۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

A ranar da Allah zai tashe su gaba xaya, sannan Ya ba su labarin abin da suka aikata. Allah Ya qididdige shi, su kuwa sun manta shi. Allah kuwa Mai ganin kowane abu ne



السورة: Suratul Mujadila

الآية : 18

يَوۡمَ يَبۡعَثُهُمُ ٱللَّهُ جَمِيعٗا فَيَحۡلِفُونَ لَهُۥ كَمَا يَحۡلِفُونَ لَكُمۡ وَيَحۡسَبُونَ أَنَّهُمۡ عَلَىٰ شَيۡءٍۚ أَلَآ إِنَّهُمۡ هُمُ ٱلۡكَٰذِبُونَ

A ranar da Allah zai tashe su baki xaya sai su rantse Masa kamar yadda suke rantse muku, su kuma riqa tsammanin su sun yi wani abu (mai amfani). Ku saurara, lalle kam su ne maqaryata



السورة: Suratul Hashr

الآية : 24

هُوَ ٱللَّهُ ٱلۡخَٰلِقُ ٱلۡبَارِئُ ٱلۡمُصَوِّرُۖ لَهُ ٱلۡأَسۡمَآءُ ٱلۡحُسۡنَىٰۚ يُسَبِّحُ لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Shi ne Allah Mahalicci, Mai qagawa Mai surantawa[1]; Yana da sunaye mafiya kyau. Duk abin da yake cikin sammai da qasa yana tsarkake Shi; kuma Shi Mabuwayi ne, Mai hikima


1- Watau mai suranta kamannin abin da ya halitta yadda ya ga dama.


السورة: Suratut Taghabun

الآية : 2

هُوَ ٱلَّذِي خَلَقَكُمۡ فَمِنكُمۡ كَافِرٞ وَمِنكُم مُّؤۡمِنٞۚ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٌ

Shi ne Wanda Ya halicce ku, don haka daga cikinku akwai kafiri, daga cikinku kuma akwai mumini. Allah kuwa Mai ganin abin da kuke aikatawa ne



السورة: Suratut Taghabun

الآية : 3

خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّ وَصَوَّرَكُمۡ فَأَحۡسَنَ صُوَرَكُمۡۖ وَإِلَيۡهِ ٱلۡمَصِيرُ

Ya halicci sammai da qasa da gaskiya, kuma Ya suranta ku, sannan Ya kyautata surorinku; zuwa gare Shi ne kuma makomarku take



السورة: Suratut Taghabun

الآية : 7

زَعَمَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَن لَّن يُبۡعَثُواْۚ قُلۡ بَلَىٰ وَرَبِّي لَتُبۡعَثُنَّ ثُمَّ لَتُنَبَّؤُنَّ بِمَا عَمِلۡتُمۡۚ وَذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ يَسِيرٞ

Waxanda suka kafirta sun riya cewa ba za a tashe su ba har abada. Ka ce: “A’a, na rantse da Ubangijina tabbas za a tashe ku, sannan kuma tabbas za a ba ku labarin abin da kuka aikata. Wannan kuwa mai sauqi ne a wurin Allah



السورة: Suratux Xalaq

الآية : 12

ٱللَّهُ ٱلَّذِي خَلَقَ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖ وَمِنَ ٱلۡأَرۡضِ مِثۡلَهُنَّۖ يَتَنَزَّلُ ٱلۡأَمۡرُ بَيۡنَهُنَّ لِتَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ وَأَنَّ ٱللَّهَ قَدۡ أَحَاطَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عِلۡمَۢا

Allah ne Wanda Ya halicci sammai bakwai, qasa ma Ya halicci kwatankwacinsu (watau sammai), umarni yana sauka a tsakaninsu, don ku san cewa, Allah Mai iko ne a kan komai, kuma haqiqa Allah iliminsa ya kewaye kowane abu



السورة: Suratul Mulk

الآية : 2

ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلۡمَوۡتَ وَٱلۡحَيَوٰةَ لِيَبۡلُوَكُمۡ أَيُّكُمۡ أَحۡسَنُ عَمَلٗاۚ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡغَفُورُ

Wanda Ya halicci mutuwa da rayuwa don Ya jarraba ku (Ya bayyana) wane ne a cikinku ya fi kyakkyawan aiki? Shi kuma Mabuwayi ne, Mai gafara



السورة: Suratul Mulk

الآية : 3

ٱلَّذِي خَلَقَ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖ طِبَاقٗاۖ مَّا تَرَىٰ فِي خَلۡقِ ٱلرَّحۡمَٰنِ مِن تَفَٰوُتٖۖ فَٱرۡجِعِ ٱلۡبَصَرَ هَلۡ تَرَىٰ مِن فُطُورٖ

Wanda Ya halicci sammai bakwai hawa-hawa; ba za ka ga wata tangarxa cikin halittar (Allah) Mai rahama ba. Ka maimaita dubanka, shin za ka ga wata tsaga?



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 3

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ

Yanzu mutum yana tsammanin ba za Mu tattara qasusuwansa ba?



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 4

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ

E, (Mu) Masu iko ne a kan Mu daidaita gavovin yatsunsa



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 37

أَلَمۡ يَكُ نُطۡفَةٗ مِّن مَّنِيّٖ يُمۡنَىٰ

Shin bai kasance wani xigo na maniyyi da ake zuba shi (a mahaifa) ba?



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 38

ثُمَّ كَانَ عَلَقَةٗ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ

Sannan ya zama gudan jini sannan (Allah) Ya halicce (shi) sai Ya daidaita (shi)?



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 39

فَجَعَلَ مِنۡهُ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ

Sannan Ya halicci dangi biyu daga gare shi, namiji da mace?



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 40

أَلَيۡسَ ذَٰلِكَ بِقَٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحۡـِۧيَ ٱلۡمَوۡتَىٰ

Yanzu wannan bai zama Mai iko a kan ya raya matattu ba?



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 27

ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا

Yanzu ku ne halittarku ta fi tsanani ko kuwa sama wadda Shi ne Ya gina ta?



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 28

رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا

Ya xaukaka rufinta Ya kuma daidaita ta[1]


1- Watau ya zama babu wata varaka ko tsagewa ko wani aibi tare da ita.


السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 29

وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا

Ya lulluve darenta da duhu Ya kuma fitar da hasken hantsinta



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 30

وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

Qasa kuma bayan haka Ya shimfixa ta



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 31

أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا

Ya fitar da ruwanta da makiyayarta daga gare ta



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 32

وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا

Duwatsu kuma Ya kafa su



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 33

مَتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ

Don jin daxinku da na dabbobinku



السورة: Suratul Infixar

الآية : 7

ٱلَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ

Wanda Ya halicce ka Ya kuma daidaita ka Ya miqar da kai[1]?


1- Watau ya lura da girman ni’imar da ya yi masa yayin da bai yi masa irin halittar jaki ba ko ta biri ko ta kare.


السورة: Suratul Infixar

الآية : 8

فِيٓ أَيِّ صُورَةٖ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ

Ya harhaxa ka cikin irin surar da Ya ga dama?



السورة: Suratul Buruj

الآية : 13

إِنَّهُۥ هُوَ يُبۡدِئُ وَيُعِيدُ

Lalle Shi ne Yake farar (da komai) Yake kuma dawo (da shi)



السورة: Suratux Xariq

الآية : 8

إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٞ

Lalle Shi (Allah) Mai iko ne a kan dawo da shi