السورة: Suratul Qamar

الآية : 55

فِي مَقۡعَدِ صِدۡقٍ عِندَ مَلِيكٖ مُّقۡتَدِرِۭ

A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko



السورة: Suratur Rahman

الآية : 46

وَلِمَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ

Duk wanda kuwa ya ji tsoron tsayuwa (gaban) Ubangijinsa yana da Aljanna biyu



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 10

وَٱلسَّـٰبِقُونَ ٱلسَّـٰبِقُونَ

Da kuma masu rige-rige (zuwa alheri)



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 11

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلۡمُقَرَّبُونَ

Waxannan su ne makusanta



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 12

فِي جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

A cikin gidajen Aljanna na ni’ima



السورة: Suratul Qalam

الآية : 34

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

Lalle masu taqawa suna da gidajen Aljannar ni’ima a wurin Ubangijinsu



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 23

ٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ دَآئِمُونَ

Waxanda suke masu dawwama a kan sallarsu



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 24

وَٱلَّذِينَ فِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ مَّعۡلُومٞ

Waxanda kuma suke akwai haqqi sananne a cikin dukiyoyinsu



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 25

لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ

Ga mai roqo da wanda ake hana wa (saboda ba ya roqo)



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 26

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

Waxanda kuma suke gaskata ranar sakamako



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 27

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنۡ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشۡفِقُونَ

Waxanda kuma suke tsoron azabar Ubangijinsu



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 28

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمۡ غَيۡرُ مَأۡمُونٖ

Lalle azabar Ubangijinsu ba abar amincewa ba ce



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 29

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِفُرُوجِهِمۡ حَٰفِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye al’aurarsu (daga yin zina)



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 30

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ

Sai a wajan matayensu ko kuma qwarqarorinsu; to su a nan ba ababen zargi ba ne



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 31

فَمَنِ ٱبۡتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡعَادُونَ

To duk wanda ya nemi (wani abu) bayan wannan, to waxannan su ne masu qetare iyaka



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 32

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِأَمَٰنَٰتِهِمۡ وَعَهۡدِهِمۡ رَٰعُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye amanoninsu da alqawuransu



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 33

وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَٰدَٰتِهِمۡ قَآئِمُونَ

Waxanda kuma suke tsai da shaidarsu



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 34

وَٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ يُحَافِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye sallolinsu



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 35

أُوْلَـٰٓئِكَ فِي جَنَّـٰتٖ مُّكۡرَمُونَ

Waxannan su ne waxanda ake girmamawa cikin gidajen Aljanna



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 41

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي ظِلَٰلٖ وَعُيُونٖ

Lalle masu taqawa suna cikin inuwoyi da idanuwan ruwa



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 42

وَفَوَٰكِهَ مِمَّا يَشۡتَهُونَ

Da kuma ababan marmari daga abin da suke sha’awa



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 43

كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ هَنِيٓـَٔۢا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Ku ci kuma ku sha kuna masu farin ciki saboda abin da kuka kasance kuna aikatawa



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 44

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 40

وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ

Duk wanda kuma ya ji tsoron tsayuwa gaban Ubangijinsa, ya kuma hana zuciya bin abin da take so



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 41

فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle Aljanna ita ce makoma



السورة: Suratul Muxaffifin

الآية : 22

إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٍ

Lalle masu biyayya tabbas suna cikin ni’ima



السورة: Suratul Muxaffifin

الآية : 23

عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ

A kan gadaje suna kallo



السورة: Suratul Muxaffifin

الآية : 24

تَعۡرِفُ فِي وُجُوهِهِمۡ نَضۡرَةَ ٱلنَّعِيمِ

Za ka gane hasken ni’ima a fuskokinsu[1]


1- Watau fuskokinsu suna sheqi da annuri.


السورة: Suratul Buruj

الآية : 11

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡكَبِيرُ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. Wannan kuwa shi ne babban rabo



السورة: Suratul Fajr

الآية : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa