ٱلَّذِينَ يَجۡتَنِبُونَ كَبَـٰٓئِرَ ٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡفَوَٰحِشَ إِلَّا ٱللَّمَمَۚ إِنَّ رَبَّكَ وَٰسِعُ ٱلۡمَغۡفِرَةِۚ هُوَ أَعۡلَمُ بِكُمۡ إِذۡ أَنشَأَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ وَإِذۡ أَنتُمۡ أَجِنَّةٞ فِي بُطُونِ أُمَّهَٰتِكُمۡۖ فَلَا تُزَكُّوٓاْ أَنفُسَكُمۡۖ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَنِ ٱتَّقَىٰٓ
(Su ne) waxanda suke nisantar manya-manyan zunubai da munanan ayyukan savo, sai dai ‘yan qananan zunubai. Lalle Ubangijinka Mayalwacin gafara ne. Shi ne Ya fi sanin ku, tun sanda Ya halicce ku daga qasa, sai ga ku kun zama ‘yan tayi a cikin cikin iyayenku mata; to kada ku tsarkake kanku; Shi ne Ya fi sanin wanda ya fi taqawa
خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِن صَلۡصَٰلٖ كَٱلۡفَخَّارِ
Ya halicci mutum daga busasshen tavo kamar kasko
نَحۡنُ خَلَقۡنَٰكُمۡ فَلَوۡلَا تُصَدِّقُونَ
Mu ne Muka halicce ku, me ya sa ba kwa gaskatawa?
أَفَرَءَيۡتُم مَّا تُمۡنُونَ
Ba kwa ganin maniyyi da kuke zubawa
ءَأَنتُمۡ تَخۡلُقُونَهُۥٓ أَمۡ نَحۡنُ ٱلۡخَٰلِقُونَ
Shin ku ne kuke halittar sa, ko kuwa Mu ne Masu halittar?
وَٱللَّهُ أَنۢبَتَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ نَبَاتٗا
“Allah ne kuma Ya tsiro da ku daga qasa a tsirowa (ta halitta)[1]
1- Watau ya halicce su daga qasa ta hanyar halittar babansu Annabi Adamu (), suna kuma cin abin da qasar ta tsiro da shi.
أَلَمۡ يَكُ نُطۡفَةٗ مِّن مَّنِيّٖ يُمۡنَىٰ
Shin bai kasance wani xigo na maniyyi da ake zuba shi (a mahaifa) ba?
ثُمَّ كَانَ عَلَقَةٗ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ
Sannan ya zama gudan jini sannan (Allah) Ya halicce (shi) sai Ya daidaita (shi)?
فَجَعَلَ مِنۡهُ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ
Sannan Ya halicci dangi biyu daga gare shi, namiji da mace?
هَلۡ أَتَىٰ عَلَى ٱلۡإِنسَٰنِ حِينٞ مِّنَ ٱلدَّهۡرِ لَمۡ يَكُن شَيۡـٔٗا مَّذۡكُورًا
Haqiqa wani yanki na zamani ya zo wa mutum yayin da bai zama wani abin ambato ba[1]
1- Watau babu shi gaba xaya, babu kuma wanda ya san shi.
إِنَّا خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ مِن نُّطۡفَةٍ أَمۡشَاجٖ نَّبۡتَلِيهِ فَجَعَلۡنَٰهُ سَمِيعَۢا بَصِيرًا
Lalle Mun halicci mutum daga maniyyi gamin-gambiza[1] don Mu jarrabe shi, sai Muka sanya shi mai ji mai gani
1- Watau tsakanin na namiji da na mace.
أَلَمۡ نَخۡلُقكُّم مِّن مَّآءٖ مَّهِينٖ
Yanzu ba Mu halicce ku daga wani wulaqantaccen ruwa ba?
فَجَعَلۡنَٰهُ فِي قَرَارٖ مَّكِينٍ
Sannan Muka sanya shi cikin matabbata mai aminci?
إِلَىٰ قَدَرٖ مَّعۡلُومٖ
Zuwa wani lokaci sananne?
فَقَدَرۡنَا فَنِعۡمَ ٱلۡقَٰدِرُونَ
Sannan Muka qaddara (komai ta yadda ya dace)? To madalla da Masu qaddarawa
مِنۡ أَيِّ شَيۡءٍ خَلَقَهُۥ
Shin daga wane abu ne (Allah) Ya halicce shi?
مِن نُّطۡفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ
Daga maniyyi ne Ya halicce shi, sannan Ya qaddara shi (matakai a halitta)
فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ مِمَّ خُلِقَ
To mutum ya duba mana, daga me aka halicce shi?
خُلِقَ مِن مَّآءٖ دَافِقٖ
An halicce shi ne daga wani ruwa mai ingizar juna[1]
1- Watau maniyyi.
يَخۡرُجُ مِنۢ بَيۡنِ ٱلصُّلۡبِ وَٱلتَّرَآئِبِ
Mai fita daga tsakanin tsatso da karankarma[1]
1- Watau daga tsakanin qashin bayan namiji da qasusuwan qirjinsa.
خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِنۡ عَلَقٍ
Ya halicci mutum daga gudan jini[1]
1- Watau bayan yana xigon maniyyi.