السورة: Suratul Baqara

الآية : 195

وَأَنفِقُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَلَا تُلۡقُواْ بِأَيۡدِيكُمۡ إِلَى ٱلتَّهۡلُكَةِ وَأَحۡسِنُوٓاْۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Kuma ku ciyar da dukiyoyinku a hanyar Allah, kuma kada ku jefa kawunanku zuwa ga halaka, kuma ku kyautata; lalle Allah Yana son masu kyautatawa



السورة: Suratul Baqara

الآية : 222

وَيَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلۡمَحِيضِۖ قُلۡ هُوَ أَذٗى فَٱعۡتَزِلُواْ ٱلنِّسَآءَ فِي ٱلۡمَحِيضِ وَلَا تَقۡرَبُوهُنَّ حَتَّىٰ يَطۡهُرۡنَۖ فَإِذَا تَطَهَّرۡنَ فَأۡتُوهُنَّ مِنۡ حَيۡثُ أَمَرَكُمُ ٱللَّهُۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلتَّوَّـٰبِينَ وَيُحِبُّ ٱلۡمُتَطَهِّرِينَ

Kuma suna tambayar ka game da jinin haila. Ka ce:  “Shi cuta ne, don haka ku qaurace wa mata a (kwanakin) haila, kuma kada ku kusance su har sai sun tsarkaka. To idan suka yi tsarki, sai ku zo musu ta inda Allah Ya umarce ku. Lalle Allah Yana son masu yawan tuba, kuma Yana son masu tsarki.”



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 31

قُلۡ إِن كُنتُمۡ تُحِبُّونَ ٱللَّهَ فَٱتَّبِعُونِي يُحۡبِبۡكُمُ ٱللَّهُ وَيَغۡفِرۡ لَكُمۡ ذُنُوبَكُمۡۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ka ce: “In kun kasance kuna son Allah, to ku yi mini biyayya, sai Allah Ya so ku, kuma Ya gafarta muku zunubanku. Kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin qai.”



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 76

بَلَىٰۚ مَنۡ أَوۡفَىٰ بِعَهۡدِهِۦ وَٱتَّقَىٰ فَإِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُتَّقِينَ

Ba haka ba ne, duk wanda ya cika alqawarinsa, kuma ya tsare dokar Allah, to lalle Allah Yana son masu taqawa



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 134

ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ فِي ٱلسَّرَّآءِ وَٱلضَّرَّآءِ وَٱلۡكَٰظِمِينَ ٱلۡغَيۡظَ وَٱلۡعَافِينَ عَنِ ٱلنَّاسِۗ وَٱللَّهُ يُحِبُّ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

(Su ne) waxanda suke ciyarwa a cikin halin yalwa da halin qunci, kuma masu voye fushi kuma masu yin afuwa ga mutane. Allah kuwa Yana son masu kyautatawa



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 146

وَكَأَيِّن مِّن نَّبِيّٖ قَٰتَلَ مَعَهُۥ رِبِّيُّونَ كَثِيرٞ فَمَا وَهَنُواْ لِمَآ أَصَابَهُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَمَا ضَعُفُواْ وَمَا ٱسۡتَكَانُواْۗ وَٱللَّهُ يُحِبُّ ٱلصَّـٰبِرِينَ

Kuma sau da yawa an sami wani annabi (daga cikin annabawa), mabiya masu yawa sun yi yaqi tare da shi, amma ba su tava yin rauni ba saboda abin da ya same su a tafarkin Allah, kuma ba su tava yin ragwanci ba, kuma ba su tava miqa wuya ba. Kuma Allah Yana son masu haquri



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 148

فَـَٔاتَىٰهُمُ ٱللَّهُ ثَوَابَ ٱلدُّنۡيَا وَحُسۡنَ ثَوَابِ ٱلۡأٓخِرَةِۗ وَٱللَّهُ يُحِبُّ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Sai Allah Ya ba su ladan duniya da kyakkyawan lada na lahira. Kuma Allah Yana son masu kyautatawa



السورة: Suratu Ali-Imran

الآية : 159

فَبِمَا رَحۡمَةٖ مِّنَ ٱللَّهِ لِنتَ لَهُمۡۖ وَلَوۡ كُنتَ فَظًّا غَلِيظَ ٱلۡقَلۡبِ لَٱنفَضُّواْ مِنۡ حَوۡلِكَۖ فَٱعۡفُ عَنۡهُمۡ وَٱسۡتَغۡفِرۡ لَهُمۡ وَشَاوِرۡهُمۡ فِي ٱلۡأَمۡرِۖ فَإِذَا عَزَمۡتَ فَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُتَوَكِّلِينَ

To saboda rahama ta musamman daga Allah, sai ka zamo mai tausasawa gare su; in da kuwa ka kasance mai kaushin mu’amala, mai qeqasasshiyar zuciya ne, to da sun watse sun bar ka. To ka yi musu afuwa, kuma ka nema musu gafara, kuma ka nemi shawararsu cikin duk lamura; amma idan ka riga ka qulla niyya, to ka dogara ga Allah. Lalle Allah Yana son masu dogara a gare Shi



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 13

فَبِمَا نَقۡضِهِم مِّيثَٰقَهُمۡ لَعَنَّـٰهُمۡ وَجَعَلۡنَا قُلُوبَهُمۡ قَٰسِيَةٗۖ يُحَرِّفُونَ ٱلۡكَلِمَ عَن مَّوَاضِعِهِۦ وَنَسُواْ حَظّٗا مِّمَّا ذُكِّرُواْ بِهِۦۚ وَلَا تَزَالُ تَطَّلِعُ عَلَىٰ خَآئِنَةٖ مِّنۡهُمۡ إِلَّا قَلِيلٗا مِّنۡهُمۡۖ فَٱعۡفُ عَنۡهُمۡ وَٱصۡفَحۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Saboda yadda suke warware alqawarin da aka yi da su, sai Muka la’ance su, kuma Muka sanya zukatansu suka zamo qeqasassu; suna jirkita magana daga wurinta, kuma sun bar wani rabo na abin da aka yi musu wa’azi da shi. Kuma ba za ka gushe ba kana ganin ha’inci daga gare su, sai ‘yan kaxan daga cikinsu. To sai ka yi musu afuwa, kuma ka kawar da kai, lalle Allah Yana son masu kyautatawa



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 42

سَمَّـٰعُونَ لِلۡكَذِبِ أَكَّـٰلُونَ لِلسُّحۡتِۚ فَإِن جَآءُوكَ فَٱحۡكُم بَيۡنَهُمۡ أَوۡ أَعۡرِضۡ عَنۡهُمۡۖ وَإِن تُعۡرِضۡ عَنۡهُمۡ فَلَن يَضُرُّوكَ شَيۡـٔٗاۖ وَإِنۡ حَكَمۡتَ فَٱحۡكُم بَيۡنَهُم بِٱلۡقِسۡطِۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُقۡسِطِينَ

(Su ne) masu yawan sauraron qarya, masu yawan cin haram. Don haka idan sun zo maka, to ka yi musu hukunci, ko ka kau da kai daga gare su; idan kuwa ka kawar da kai daga gare su, to ba za su cutar da kai da komai ba; idan kuwa za ka yi hukuncin, to ka yi hukunci tsakaninsu da adalci. Lalle Allah Yana son masu adalci



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 54

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَن يَرۡتَدَّ مِنكُمۡ عَن دِينِهِۦ فَسَوۡفَ يَأۡتِي ٱللَّهُ بِقَوۡمٖ يُحِبُّهُمۡ وَيُحِبُّونَهُۥٓ أَذِلَّةٍ عَلَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ أَعِزَّةٍ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ يُجَٰهِدُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَلَا يَخَافُونَ لَوۡمَةَ لَآئِمٖۚ ذَٰلِكَ فَضۡلُ ٱللَّهِ يُؤۡتِيهِ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ وَٰسِعٌ عَلِيمٌ

Ya ku waxanda suka yi imani, duk wanda ya yi ridda daga cikinku, ya bar addininsa, to (ya sani) Allah zai kawo waxansu mutane da Yake son su suna son Sa, suna masu qasqantar da kai ga muminai, suna masu nuna wa kafirai isa, suna yin jihadi don xaukaka kalmar Allah, kuma ba sa jin tsoron zargin wani mai zargi. Wannan falalar Allah ce da Yake bayar da ita ga wanda Ya ga dama. Kuma Allah Mayalwaci ne, Masani



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 93

لَيۡسَ عَلَى ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ جُنَاحٞ فِيمَا طَعِمُوٓاْ إِذَا مَا ٱتَّقَواْ وَّءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ ثُمَّ ٱتَّقَواْ وَّءَامَنُواْ ثُمَّ ٱتَّقَواْ وَّأَحۡسَنُواْۚ وَٱللَّهُ يُحِبُّ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Babu wani laifi a kan waxanda suka yi imani, kuma suka yi aiki nagari cikin abin da suka tava sha (na giya a baya), in dai sun yi taqawa, kuma sun yi imani, kuma sun aikata aiki nagari, sannan suka yi taqawa da imani, sannan suka yi taqawa kuma suka kyautata. Kuma Allah Yana son masu kyautatawa



السورة: Suratut Tauba

الآية : 4

إِلَّا ٱلَّذِينَ عَٰهَدتُّم مِّنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ ثُمَّ لَمۡ يَنقُصُوكُمۡ شَيۡـٔٗا وَلَمۡ يُظَٰهِرُواْ عَلَيۡكُمۡ أَحَدٗا فَأَتِمُّوٓاْ إِلَيۡهِمۡ عَهۡدَهُمۡ إِلَىٰ مُدَّتِهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُتَّقِينَ

Sai fa waxannan mushrikan da kuka yi alqawari da su sannan kuma ba su rage muku wani abu ba (daga alqawarin), ba su kuma taimaka wa wani a kanku ba, to sai ku cika musu alqawarinsu har zuwa lokacinsu (da kuka ayyana). Lalle Allah Yana son masu taqawa



السورة: Suratut Tauba

الآية : 7

كَيۡفَ يَكُونُ لِلۡمُشۡرِكِينَ عَهۡدٌ عِندَ ٱللَّهِ وَعِندَ رَسُولِهِۦٓ إِلَّا ٱلَّذِينَ عَٰهَدتُّمۡ عِندَ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِۖ فَمَا ٱسۡتَقَٰمُواْ لَكُمۡ فَٱسۡتَقِيمُواْ لَهُمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُتَّقِينَ

Ta yaya zai yiwu a samu wani alqawari tsakanin Allah da Manzonsa da kuma mushirikai in ban da waxanda kuka yi alqawari da su a Masallaci mai alfarma? To matuqar sun tsaya muku (bisa gaskiya) sai ku ma ku tsaya musu. Lalle Allah Yana son masu taqawa



السورة: Suratut Tauba

الآية : 108

لَا تَقُمۡ فِيهِ أَبَدٗاۚ لَّمَسۡجِدٌ أُسِّسَ عَلَى ٱلتَّقۡوَىٰ مِنۡ أَوَّلِ يَوۡمٍ أَحَقُّ أَن تَقُومَ فِيهِۚ فِيهِ رِجَالٞ يُحِبُّونَ أَن يَتَطَهَّرُواْۚ وَٱللَّهُ يُحِبُّ ٱلۡمُطَّهِّرِينَ

Kada ka yi salla a cikinsa har abada. Haqiqa masallacin da aka xora harsashinsa tun daga ranar farko a kan taqawa shi ya cancanci ka yi salla a cikinsa. A cikinsa akwai wasu mazaje da suke so su tsarkaka. Allah kuwa Yana son masu tsarkaka



السورة: Suratul Fat’h

الآية : 18

۞لَّقَدۡ رَضِيَ ٱللَّهُ عَنِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ إِذۡ يُبَايِعُونَكَ تَحۡتَ ٱلشَّجَرَةِ فَعَلِمَ مَا فِي قُلُوبِهِمۡ فَأَنزَلَ ٱلسَّكِينَةَ عَلَيۡهِمۡ وَأَثَٰبَهُمۡ فَتۡحٗا قَرِيبٗا

Haqiqa Allah Ya yarda da muminai yayin da suke yi maka mubaya’a a qarqashin bishiyar[1] nan, to Allah Ya san abin da yake cikin zukatansu, sai Ya saukar musu da nutsuwa Ya kuma saka musu da buxi na kurkusa[2]


1- Su ne sahabban Annabi () kimanin su dubu da xari huxu da suka yi wa Manzon Allah () mubaya’a a Hudaibiyya a kan za su jajirce wajen yaqi tare da shi.


2- Watau buxe Khaibar a madadin rashin samun shiga garin Makka su yi umara.


السورة: Suratul Hujurat

الآية : 9

وَإِن طَآئِفَتَانِ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ ٱقۡتَتَلُواْ فَأَصۡلِحُواْ بَيۡنَهُمَاۖ فَإِنۢ بَغَتۡ إِحۡدَىٰهُمَا عَلَى ٱلۡأُخۡرَىٰ فَقَٰتِلُواْ ٱلَّتِي تَبۡغِي حَتَّىٰ تَفِيٓءَ إِلَىٰٓ أَمۡرِ ٱللَّهِۚ فَإِن فَآءَتۡ فَأَصۡلِحُواْ بَيۡنَهُمَا بِٱلۡعَدۡلِ وَأَقۡسِطُوٓاْۖ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُقۡسِطِينَ

Idan kuma wasu qungiyoyi biyu na muminai suka yaqi junansu sai ku yi sulhu a tsakaninsu; to idan xayarsu ta yi ta’adda a kan xayar, to sai ku yaqi wadda ta yi ta’addar har sai ta komo zuwa bin umarnin Allah. Idan ta komo sai ku yi sulhu a tsakaninsu bisa adalci, ku kuma yi adalci; lalle Allah Yana son masu adalci



السورة: Suratul Mujadila

الآية : 22

لَّا تَجِدُ قَوۡمٗا يُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ يُوَآدُّونَ مَنۡ حَآدَّ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ وَلَوۡ كَانُوٓاْ ءَابَآءَهُمۡ أَوۡ أَبۡنَآءَهُمۡ أَوۡ إِخۡوَٰنَهُمۡ أَوۡ عَشِيرَتَهُمۡۚ أُوْلَـٰٓئِكَ كَتَبَ فِي قُلُوبِهِمُ ٱلۡإِيمَٰنَ وَأَيَّدَهُم بِرُوحٖ مِّنۡهُۖ وَيُدۡخِلُهُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ رَضِيَ ٱللَّهُ عَنۡهُمۡ وَرَضُواْ عَنۡهُۚ أُوْلَـٰٓئِكَ حِزۡبُ ٱللَّهِۚ أَلَآ إِنَّ حِزۡبَ ٱللَّهِ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

Ba za ka tava samun wasu mutane da suke yin imani da Allah da ranar lahira ba, su riqa qaunar waxanda suke gaba da Allah da Manzonsa, ko da kuwa sun kasance iyayensu ne ko ‘ya’yansu ko ‘yan’uwansu ko kuma danginsu. Waxannan Allah Ya rubuta imani a cikin zukatansu, Ya kuma qarfafe su da wani ruhi daga wurinsa[1]; zai kuma shigar da su gidajen Aljanna (waxanda) qoramu suke gudana ta qarqashinsu, madawwama a cikinsu. Allah Ya yarda da su, su ma sun yarda da Shi. Waxannan ne qungiyar Allah. Ku saurara, lalle qungiyar Allah su ne masu samun babban rabo


1- Watau zai qarfafe su da wata hujja daga wurinsa da haske.


السورة: Suratul Mumtahana

الآية : 8

لَّا يَنۡهَىٰكُمُ ٱللَّهُ عَنِ ٱلَّذِينَ لَمۡ يُقَٰتِلُوكُمۡ فِي ٱلدِّينِ وَلَمۡ يُخۡرِجُوكُم مِّن دِيَٰرِكُمۡ أَن تَبَرُّوهُمۡ وَتُقۡسِطُوٓاْ إِلَيۡهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلۡمُقۡسِطِينَ

Allah bai hana ku ba game da waxanda ba su yaqe ku don addini ba, ba su kuma fitar da ku daga gidajenku ba, kan ku kyautata musu, ku kuma yi musu adalci. Lalle Allah Yana son masu adalci



السورة: Suratus Saff 

الآية : 4

إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلَّذِينَ يُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِهِۦ صَفّٗا كَأَنَّهُم بُنۡيَٰنٞ مَّرۡصُوصٞ

Lalle Allah Yana son waxanda suke yin yaqi dominsa sahu-sahu kai ka ce su gini ne wanda yake xamfare da juna