قَالَ إِنَّ فِيهَا لُوطٗاۚ قَالُواْ نَحۡنُ أَعۡلَمُ بِمَن فِيهَاۖ لَنُنَجِّيَنَّهُۥ وَأَهۡلَهُۥٓ إِلَّا ٱمۡرَأَتَهُۥ كَانَتۡ مِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ
Sai (Ibrahimu) ya ce: “Lalle Luxu yana cikinta”. Sai suka ce: “Mu muka fi sanin waxanda suke cikinta; tabbas za mu tserar da shi tare da iyalinsa, sai matarsa kawai da ta kasance cikin waxanda za su yi saura (a hallaka su tare)”
وَلَمَّآ أَن جَآءَتۡ رُسُلُنَا لُوطٗا سِيٓءَ بِهِمۡ وَضَاقَ بِهِمۡ ذَرۡعٗاۖ وَقَالُواْ لَا تَخَفۡ وَلَا تَحۡزَنۡ إِنَّا مُنَجُّوكَ وَأَهۡلَكَ إِلَّا ٱمۡرَأَتَكَ كَانَتۡ مِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ
Lokacin kuma da manzanninmu suka zo wa Luxu, sai ya yi baqin ciki da zuwansu, zuciyarsa kuma ta quntata saboda su[1], sai suka ce da shi: “Kada ka ji tsoro, kuma kada ka damu; lalle mu masu tserar da kai ne tare da iyalinka, sai matarka kawai da ta kasance cikin waxanda za su yi saura (a hallaka su tare)
1- Domin jiye musu tsoron mugun halin mutanensa musamman saboda mala’ikun sun zo a cikin kamanni na mutane maza.
إِنَّا مُنزِلُونَ عَلَىٰٓ أَهۡلِ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةِ رِجۡزٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ بِمَا كَانُواْ يَفۡسُقُونَ
“Lalle mu masu saukar da azaba ce daga sama a kan mutanen wannan alqaryar saboda abin da suka kasance suna aikatawa na fasiqanci.”
وَإِنَّ لُوطٗا لَّمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Lalle kuma Luxu tabbas yana daga cikin manzanni
إِذۡ نَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ
(Ka tuna) sanda Muka tserar da shi tare da iyalinsa baki xaya
إِلَّا عَجُوزٗا فِي ٱلۡغَٰبِرِينَ
Sai dai wata tsohuwa (wato matarsa) da take cikin halakakku
ثُمَّ دَمَّرۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ
Sannan Muka hallakar da sauran
وَإِنَّكُمۡ لَتَمُرُّونَ عَلَيۡهِم مُّصۡبِحِينَ
Kuma lalle ku[1] tabbas kuna wucewa ta wajan (gidajensu) da asussuba
1- Watau ku mutanen Makka.
وَبِٱلَّيۡلِۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ
Da kuma cikin dare. Yanzu ba kwa hankalta ba?
كَذَّبَتۡ قَوۡمُ لُوطِۭ بِٱلنُّذُرِ
Mutanen Luxu sun qaryata gargaxi
إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ حَاصِبًا إِلَّآ ءَالَ لُوطٖۖ نَّجَّيۡنَٰهُم بِسَحَرٖ
Lalle Mun aika musu da iska cike da duwatsu (ta hallaka su), sai dai iyalin Luxu kaxai Muka tserar da su a lokacin asuba
نِّعۡمَةٗ مِّنۡ عِندِنَاۚ كَذَٰلِكَ نَجۡزِي مَن شَكَرَ
(Wannan) ni’ima ce daga wurinmu. Kamar haka Muke saka wa wanda ya yi godiya
وَلَقَدۡ أَنذَرَهُم بَطۡشَتَنَا فَتَمَارَوۡاْ بِٱلنُّذُرِ
Kuma haqiqa ya tsoratar da su irin damqarmu, sai suka yi jayayya da gargaxin (da ya yi musu)
وَلَقَدۡ رَٰوَدُوهُ عَن ضَيۡفِهِۦ فَطَمَسۡنَآ أَعۡيُنَهُمۡ فَذُوقُواْ عَذَابِي وَنُذُرِ
Haqiqa kuma sun nemi baqinsa[1] da lalata, sai Muka shafe idanuwansu, (Muka ce da su): “Sai ku xanxani azabata da gargaxina.
1- Su ne mala’iku da suka zo masa a siffar mutane matasa kyawawa.
وَلَقَدۡ صَبَّحَهُم بُكۡرَةً عَذَابٞ مُّسۡتَقِرّٞ
Haqiqa kuma azaba matabbaciya ta yi musu sammako da asuba.
فَذُوقُواْ عَذَابِي وَنُذُرِ
Saboda haka ku xanxani azabata da gargaxina.”