السورة: Suratul Ankabut

الآية : 32

قَالَ إِنَّ فِيهَا لُوطٗاۚ قَالُواْ نَحۡنُ أَعۡلَمُ بِمَن فِيهَاۖ لَنُنَجِّيَنَّهُۥ وَأَهۡلَهُۥٓ إِلَّا ٱمۡرَأَتَهُۥ كَانَتۡ مِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai (Ibrahimu) ya ce: “Lalle Luxu yana cikinta”. Sai suka ce: “Mu muka fi sanin waxanda suke cikinta; tabbas za mu tserar da shi tare da iyalinsa, sai matarsa kawai da ta kasance cikin waxanda za su yi saura (a hallaka su tare)”



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 33

وَلَمَّآ أَن جَآءَتۡ رُسُلُنَا لُوطٗا سِيٓءَ بِهِمۡ وَضَاقَ بِهِمۡ ذَرۡعٗاۖ وَقَالُواْ لَا تَخَفۡ وَلَا تَحۡزَنۡ إِنَّا مُنَجُّوكَ وَأَهۡلَكَ إِلَّا ٱمۡرَأَتَكَ كَانَتۡ مِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ

Lokacin kuma da manzanninmu suka zo wa Luxu, sai ya yi baqin ciki da zuwansu, zuciyarsa kuma ta quntata saboda su[1], sai suka ce da shi: “Kada ka ji tsoro, kuma kada ka damu; lalle mu masu tserar da kai ne tare da iyalinka, sai matarka kawai da ta kasance cikin waxanda za su yi saura (a hallaka su tare)


1- Domin jiye musu tsoron mugun halin mutanensa musamman saboda mala’ikun sun zo a cikin kamanni na mutane maza.


السورة: Suratul Ankabut

الآية : 34

إِنَّا مُنزِلُونَ عَلَىٰٓ أَهۡلِ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةِ رِجۡزٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ بِمَا كَانُواْ يَفۡسُقُونَ

“Lalle mu masu saukar da azaba ce daga sama a kan mutanen wannan alqaryar saboda abin da suka kasance suna aikatawa na fasiqanci.”



السورة: Suratus Saffat

الآية : 133

وَإِنَّ لُوطٗا لَّمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Lalle kuma Luxu tabbas yana daga cikin manzanni



السورة: Suratus Saffat

الآية : 134

إِذۡ نَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

(Ka tuna) sanda Muka tserar da shi tare da iyalinsa baki xaya



السورة: Suratus Saffat

الآية : 135

إِلَّا عَجُوزٗا فِي ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai dai wata tsohuwa (wato matarsa) da take cikin halakakku



السورة: Suratus Saffat

الآية : 136

ثُمَّ دَمَّرۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka hallakar da sauran



السورة: Suratus Saffat

الآية : 137

وَإِنَّكُمۡ لَتَمُرُّونَ عَلَيۡهِم مُّصۡبِحِينَ

Kuma lalle ku[1] tabbas kuna wucewa ta wajan (gidajensu) da asussuba


1- Watau ku mutanen Makka.


السورة: Suratus Saffat

الآية : 138

وَبِٱلَّيۡلِۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Da kuma cikin dare. Yanzu ba kwa hankalta ba?



السورة: Suratul Qamar

الآية : 33

كَذَّبَتۡ قَوۡمُ لُوطِۭ بِٱلنُّذُرِ

Mutanen Luxu sun qaryata gargaxi



السورة: Suratul Qamar

الآية : 34

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ حَاصِبًا إِلَّآ ءَالَ لُوطٖۖ نَّجَّيۡنَٰهُم بِسَحَرٖ

Lalle Mun aika musu da iska cike da duwatsu (ta hallaka su), sai dai iyalin Luxu kaxai Muka tserar da su a lokacin asuba



السورة: Suratul Qamar

الآية : 35

نِّعۡمَةٗ مِّنۡ عِندِنَاۚ كَذَٰلِكَ نَجۡزِي مَن شَكَرَ

(Wannan) ni’ima ce daga wurinmu. Kamar haka Muke saka wa wanda ya yi godiya



السورة: Suratul Qamar

الآية : 36

وَلَقَدۡ أَنذَرَهُم بَطۡشَتَنَا فَتَمَارَوۡاْ بِٱلنُّذُرِ

Kuma haqiqa ya tsoratar da su irin damqarmu, sai suka yi jayayya da gargaxin (da ya yi musu)



السورة: Suratul Qamar

الآية : 37

وَلَقَدۡ رَٰوَدُوهُ عَن ضَيۡفِهِۦ فَطَمَسۡنَآ أَعۡيُنَهُمۡ فَذُوقُواْ عَذَابِي وَنُذُرِ

Haqiqa kuma sun nemi baqinsa[1] da lalata, sai Muka shafe idanuwansu, (Muka ce da su): “Sai ku xanxani azabata da gargaxina.


1- Su ne mala’iku da suka zo masa a siffar mutane matasa kyawawa.


السورة: Suratul Qamar

الآية : 38

وَلَقَدۡ صَبَّحَهُم بُكۡرَةً عَذَابٞ مُّسۡتَقِرّٞ

Haqiqa kuma azaba matabbaciya ta yi musu sammako da asuba.



السورة: Suratul Qamar

الآية : 39

فَذُوقُواْ عَذَابِي وَنُذُرِ

Saboda haka ku xanxani azabata da gargaxina.”