السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 93

أَلَّا تَتَّبِعَنِۖ أَفَعَصَيۡتَ أَمۡرِي

“Ka bi ni (don ka sanar da ni)? Ko kuwa ka sava umarnina ne?”



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 94

قَالَ يَبۡنَؤُمَّ لَا تَأۡخُذۡ بِلِحۡيَتِي وَلَا بِرَأۡسِيٓۖ إِنِّي خَشِيتُ أَن تَقُولَ فَرَّقۡتَ بَيۡنَ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ وَلَمۡ تَرۡقُبۡ قَوۡلِي

(Haruna) ya ce: “Ya xan’ummata, kada ka kama mini gemuna, da kuma (gashin) kaina; lalle ni na ji tsoron ka ce (da ni): ‘Ka rarraba kan Banu-Isra’ila, ba ka kuma kiyaye maganata ba.’”



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 95

قَالَ فَمَا خَطۡبُكَ يَٰسَٰمِرِيُّ

(Musa) ya ce: “Mene ne lamarinka, ya Samiri?”



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 96

قَالَ بَصُرۡتُ بِمَا لَمۡ يَبۡصُرُواْ بِهِۦ فَقَبَضۡتُ قَبۡضَةٗ مِّنۡ أَثَرِ ٱلرَّسُولِ فَنَبَذۡتُهَا وَكَذَٰلِكَ سَوَّلَتۡ لِي نَفۡسِي

Ya ce: “Na ga abin da ba su gani ba ne[1], sai na xebi danqi daga gurbin (qasar) sawun (goxiyar) Manzon (wato Jibrilu) sannan na watsa ta (a kan xan maraqin). Kamar haka kuwa raina ya qawata mini.”


1- Watau ya ga Mala’ika Jibrilu a kan dokinsa lokacin da ya zo hallaka Fir’auna da jama’arsa.


السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 97

قَالَ فَٱذۡهَبۡ فَإِنَّ لَكَ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ أَن تَقُولَ لَا مِسَاسَۖ وَإِنَّ لَكَ مَوۡعِدٗا لَّن تُخۡلَفَهُۥۖ وَٱنظُرۡ إِلَىٰٓ إِلَٰهِكَ ٱلَّذِي ظَلۡتَ عَلَيۡهِ عَاكِفٗاۖ لَّنُحَرِّقَنَّهُۥ ثُمَّ لَنَنسِفَنَّهُۥ فِي ٱلۡيَمِّ نَسۡفًا

(Annabi Musa) ya ce: “To sai ka tafi, amma ka tabbatar cewa (sakamakonka) a rayuwar (da za ka yi) shi ne ka riqa cewa ‘la misasa’, (watau ba za ka tavu ba kuma ba za ka tava kowa ba)[1]; kuma lalle kana da qayyadajjen lokaci wanda ba za a sava maka ba; kuma ka dubi ubangijin naka wanda ka duqufa a kansa kana bauta; lalle za mu qona shi sannan tabbas za mu sheqar da shi cikin kogi.”


1- Watau ba zai iya gauraya da mutane ba; don ba zai iya tava kowa ba, ba kuma wanda zai iya tava jikinsa.


السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 98

إِنَّمَآ إِلَٰهُكُمُ ٱللَّهُ ٱلَّذِي لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۚ وَسِعَ كُلَّ شَيۡءٍ عِلۡمٗا

Abin bautarku kawai shi ne Allah wanda babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi. Ya yalwaci komai da iliminsa



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 52

۞وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنۡ أَسۡرِ بِعِبَادِيٓ إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ

Muka kuma yi wa Musa wahayi cewa: “Ka tafi cikin dare tare da bayina, lalle ku za a biyo bayanku.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 53

فَأَرۡسَلَ فِرۡعَوۡنُ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ

Sai Fir’auna ya aika zuwa birane don a tattaro (mayaqa)



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 54

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَشِرۡذِمَةٞ قَلِيلُونَ

(Fir’auna yana cewa): “Lalle waxannan tabbas ‘yan tsirarin jama’a ne



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 55

وَإِنَّهُمۡ لَنَا لَغَآئِظُونَ

“Kuma haqiqa su lalle suna fusata mu



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 56

وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَٰذِرُونَ

“Lalle kuma mu tabbas gaba xayanmu masu kwana cikin shiri ne.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 57

فَأَخۡرَجۡنَٰهُم مِّن جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

(Allah Ya ce): Sai Muka fitar da su daga gonaki da kuma idandunan ruwa



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 58

وَكُنُوزٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ

Da taskoki da kuma mazauni na alfarma



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 59

كَذَٰلِكَۖ وَأَوۡرَثۡنَٰهَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Kamar haka ne Muka gadar da su ga Banu-Isra’ila



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 60

فَأَتۡبَعُوهُم مُّشۡرِقِينَ

Sai suka bi bayansu a lokacin fitowar rana



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 61

فَلَمَّا تَرَـٰٓءَا ٱلۡجَمۡعَانِ قَالَ أَصۡحَٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدۡرَكُونَ

To lokacin da jama’ar biyu suka ga juna, sai sahabban Musa suka ce: “Lalle tabbas mu za a cim mana.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 62

قَالَ كَلَّآۖ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهۡدِينِ

(Musa) ya ce: “A’a; Ubangijina Yana tare da ni, zai kuwa shiryar da ni (hanyar tsira).”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 63

فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡبَحۡرَۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرۡقٖ كَٱلطَّوۡدِ ٱلۡعَظِيمِ

Sai Muka yi wahayi ga Musa cewa: “Ka bugi kogin da sandarka;” (da ya buge shi) sai ya dare, kowanne yanki sai ya zama kamar qaton dutse



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 64

وَأَزۡلَفۡنَا ثَمَّ ٱلۡأٓخَرِينَ

Muka kuma kusantar da waxancan (watau mutanen Fir’auna) zuwa can (kusa da kogin)



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 65

وَأَنجَيۡنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

Muka kuma tserar da Musa da waxanda suke tare da shi gaba xaya



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 66

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka nutsar da sauran mutanen (watau Fir’auna da mutanensa)



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 67

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 197

أَوَلَمۡ يَكُن لَّهُمۡ ءَايَةً أَن يَعۡلَمَهُۥ عُلَمَـٰٓؤُاْ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Yanzu bai ishe su aya ba cewa, malaman Banu- Isra’ila sun san shi?



السورة: Suratun Namli

الآية : 76

إِنَّ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانَ يَقُصُّ عَلَىٰ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ أَكۡثَرَ ٱلَّذِي هُمۡ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَ

Lalle wannan Alqur’anin yana labarta wa Banu-Isra’ila mafi yawan abin da suke savani a kansa



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 53

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡهُدَىٰ وَأَوۡرَثۡنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱلۡكِتَٰبَ

Kuma haqiqa Mun bai wa Musa shiriya, Muka kuwa gadar wa Banu-Isra’ila littafin (Attaura)



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 23

فَأَسۡرِ بِعِبَادِي لَيۡلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ

Sai (aka ce masa): “Ka tafi da bayina da daddare, lalle ku za a biyo bayanku



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 24

وَٱتۡرُكِ ٱلۡبَحۡرَ رَهۡوًاۖ إِنَّهُمۡ جُندٞ مُّغۡرَقُونَ

“Kuma ka bar kogi a tsaye cak (bayan tsallakewa); lalle su runduna ne da za a nutsar.”



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 25

كَمۡ تَرَكُواْ مِن جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

Sun bar gonaki da kuma idanuwan ruwa masu yawa



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 26

وَزُرُوعٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ

Da kuma shuke-shuke da wurin zama mai daraja



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 27

وَنَعۡمَةٖ كَانُواْ فِيهَا فَٰكِهِينَ

Da kuma kayan jin daxi da suka kasance masu ni’imtuwa da su