السورة: Suratul Baqara

الآية : 34

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ أَبَىٰ وَٱسۡتَكۡبَرَ وَكَانَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma ka tuna lokacin da Muka ce wa mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu.” Sai duk suka yi sujjada[1], in ban da Iblis, sai shi ya qi, ya kuma yi girman kai, kuma ya tabbata cikin kafirai


1- Mala’iku sun yi wa Adamu () sujjada ne don biyayya ga umarnin Allah. Ba ya halatta a Musulunci wani ya yi wa wani sujjada ba Allah ba.


السورة: Suratul A’araf

الآية : 11

وَلَقَدۡ خَلَقۡنَٰكُمۡ ثُمَّ صَوَّرۡنَٰكُمۡ ثُمَّ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ لَمۡ يَكُن مِّنَ ٱلسَّـٰجِدِينَ

Kuma lalle haqiqa Mun halicce ku, sannan kuma Muka suranta ku; sannan Muka ce wa mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu,” sai suka yi sujjada, sai Iblis ne kaxai bai kasance cikin masu sujjada ba



السورة: Suratul A’araf

الآية : 12

قَالَ مَا مَنَعَكَ أَلَّا تَسۡجُدَ إِذۡ أَمَرۡتُكَۖ قَالَ أَنَا۠ خَيۡرٞ مِّنۡهُ خَلَقۡتَنِي مِن نَّارٖ وَخَلَقۡتَهُۥ مِن طِينٖ

(Allah) Ya ce: “Me ya hana ka yin sujada lokacin da Na umarce ka?” Sai ya ce: “Ai ni na fi shi alheri; Ka halicce ni da wuta, shi kuwa Ka halicce shi da tavo.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 13

قَالَ فَٱهۡبِطۡ مِنۡهَا فَمَا يَكُونُ لَكَ أَن تَتَكَبَّرَ فِيهَا فَٱخۡرُجۡ إِنَّكَ مِنَ ٱلصَّـٰغِرِينَ

Sai Ya ce: “To ka sauka daga cikinta, bai dace gare ka ka yi girman kai a cikinta ba, don haka sai ka fita, lalle kai kana cikin qasqantattu.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 14

قَالَ أَنظِرۡنِيٓ إِلَىٰ يَوۡمِ يُبۡعَثُونَ

Sai ya ce: “Ka yi min jinkiri zuwa ranar da za a tashe su (mutane).”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 15

قَالَ إِنَّكَ مِنَ ٱلۡمُنظَرِينَ

Sai Ya ce: “Lalle kai kana cikin waxanda za a yi wa jinkiri.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 16

قَالَ فَبِمَآ أَغۡوَيۡتَنِي لَأَقۡعُدَنَّ لَهُمۡ صِرَٰطَكَ ٱلۡمُسۡتَقِيمَ

Ya ce: “Saboda vatar da ni da Ka yi, lalle sai na zaune musu tafarkinka madaidaici



السورة: Suratul A’araf

الآية : 17

ثُمَّ لَأٓتِيَنَّهُم مِّنۢ بَيۡنِ أَيۡدِيهِمۡ وَمِنۡ خَلۡفِهِمۡ وَعَنۡ أَيۡمَٰنِهِمۡ وَعَن شَمَآئِلِهِمۡۖ وَلَا تَجِدُ أَكۡثَرَهُمۡ شَٰكِرِينَ

“Sannan lalle zan zo musu ta gabansu da kuma ta bayansu da kuma ta damansu, da kuma ta hagunsu; kuma ba za Ka samu yawancinsu masu godiya ba.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 18

قَالَ ٱخۡرُجۡ مِنۡهَا مَذۡءُومٗا مَّدۡحُورٗاۖ لَّمَن تَبِعَكَ مِنۡهُمۡ لَأَمۡلَأَنَّ جَهَنَّمَ مِنكُمۡ أَجۡمَعِينَ

Ya ce: “Ka fita daga cikinta kana abin aibatawa, korarre (daga rahama); Na rantse duk wanda ya bi ka daga cikinsu, lalle zan cika Jahannama da ku gaba xaya.”



السورة: Suratul Hijr

الآية : 31

إِلَّآ إِبۡلِيسَ أَبَىٰٓ أَن يَكُونَ مَعَ ٱلسَّـٰجِدِينَ

Sai Iblis ya qi ya kasance tare da masu yin sujjadar



السورة: Suratul Hijr

الآية : 32

قَالَ يَـٰٓإِبۡلِيسُ مَا لَكَ أَلَّا تَكُونَ مَعَ ٱلسَّـٰجِدِينَ

(Allah) Ya ce: “Ya Iblis, me ka taka da ba za ka kasance tare da masu sujjada ba?”



السورة: Suratul Hijr

الآية : 33

قَالَ لَمۡ أَكُن لِّأَسۡجُدَ لِبَشَرٍ خَلَقۡتَهُۥ مِن صَلۡصَٰلٖ مِّنۡ حَمَإٖ مَّسۡنُونٖ

(Iblis) ya ce: “Ba zai yiwu ba ni in yi sujjada ga wani mutum wanda Ka halitta daga busasshen tavo mai amo na wani yumvu mai wari.”



السورة: Suratul Hijr

الآية : 34

قَالَ فَٱخۡرُجۡ مِنۡهَا فَإِنَّكَ رَجِيمٞ

(Allah) Ya ce: “To ka fita daga cikinta (Aljannar), lalle kai korarre ne (daga rahamar Allah)



السورة: Suratul Hijr

الآية : 35

وَإِنَّ عَلَيۡكَ ٱللَّعۡنَةَ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلدِّينِ

“Lalle kuma la’ana ta tabbata a kanka har zuwa ranar alqiyama.”



السورة: Suratul Hijr

الآية : 36

قَالَ رَبِّ فَأَنظِرۡنِيٓ إِلَىٰ يَوۡمِ يُبۡعَثُونَ

(Iblis) ya ce: “Ya Ubangijina Ka saurara min har zuwa ranar da za a tashe su (watau matattu).”



السورة: Suratul Hijr

الآية : 37

قَالَ فَإِنَّكَ مِنَ ٱلۡمُنظَرِينَ

(Allah) Ya ce: “To lalle kana daga cikin waxanda za a saurar musu



السورة: Suratul Hijr

الآية : 38

إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡوَقۡتِ ٱلۡمَعۡلُومِ

“Har zuwa rana mai sanannen lokaci.”



السورة: Suratul Hijr

الآية : 39

قَالَ رَبِّ بِمَآ أَغۡوَيۡتَنِي لَأُزَيِّنَنَّ لَهُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَأُغۡوِيَنَّهُمۡ أَجۡمَعِينَ

(Iblis) ya ce: “Ubangijina, saboda vatar da ni da Ka yi, to lalle kuwa zan qawata musu (varna) a bayan qasa, kuma tabbas zan vatar da su baki xaya



السورة: Suratul Hijr

الآية : 40

إِلَّا عِبَادَكَ مِنۡهُمُ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

“Sai fa bayinka zavavvu daga cikinsu.”



السورة: Suratul Hijr

الآية : 41

قَالَ هَٰذَا صِرَٰطٌ عَلَيَّ مُسۡتَقِيمٌ

(Allah) Ya ce: “Wannan hanya ce madaidaiciya, mai kaiwa gare Ni



السورة: Suratul Hijr

الآية : 42

إِنَّ عِبَادِي لَيۡسَ لَكَ عَلَيۡهِمۡ سُلۡطَٰنٌ إِلَّا مَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلۡغَاوِينَ

“Lalle bayina ba ka da wani iko a kansu, sai dai wanda ya bi ka daga vatattu



السورة: Suratul Hijr

الآية : 43

وَإِنَّ جَهَنَّمَ لَمَوۡعِدُهُمۡ أَجۡمَعِينَ

“Lalle kuma Jahannama tabbas makomarsu ce baki xaya



السورة: Suratul Hijr

الآية : 44

لَهَا سَبۡعَةُ أَبۡوَٰبٖ لِّكُلِّ بَابٖ مِّنۡهُمۡ جُزۡءٞ مَّقۡسُومٌ

“Tana da qofofi bakwai, kowacce qofa tana da wani kaso (na kafirai) sananne (da za su shiga ta nan).”



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 61

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ قَالَ ءَأَسۡجُدُ لِمَنۡ خَلَقۡتَ طِينٗا

Kuma (ka tuna) lokacin da Muka ce da mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu.” Sai suka yi sujjadar in ban da Iblis da ya ce: “Yanzu na yi sujjada ga wanda Ka halitta da tavo?”



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 62

قَالَ أَرَءَيۡتَكَ هَٰذَا ٱلَّذِي كَرَّمۡتَ عَلَيَّ لَئِنۡ أَخَّرۡتَنِ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ لَأَحۡتَنِكَنَّ ذُرِّيَّتَهُۥٓ إِلَّا قَلِيلٗا

Ya ce: “Ka gan Ka, wannan da Ka fifita shi a kaina, tabbas idan Ka jinkirta min har zuwa ranar alqiyama to lalle zan karkatar da zuriyarsa, sai dai kaxan (daga cikinsu).”



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 63

قَالَ ٱذۡهَبۡ فَمَن تَبِعَكَ مِنۡهُمۡ فَإِنَّ جَهَنَّمَ جَزَآؤُكُمۡ جَزَآءٗ مَّوۡفُورٗا

(Allah) Ya ce: “Je ka (an jinkirta maka xin), sai dai (duk) wanda ya bi ka daga cikinsu to lalle Jahannama ce sakamakonku, wanda yake sakamako ne cikakke



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 64

وَٱسۡتَفۡزِزۡ مَنِ ٱسۡتَطَعۡتَ مِنۡهُم بِصَوۡتِكَ وَأَجۡلِبۡ عَلَيۡهِم بِخَيۡلِكَ وَرَجِلِكَ وَشَارِكۡهُمۡ فِي ٱلۡأَمۡوَٰلِ وَٱلۡأَوۡلَٰدِ وَعِدۡهُمۡۚ وَمَا يَعِدُهُمُ ٱلشَّيۡطَٰنُ إِلَّا غُرُورًا

“Ka kuma yi wasa da hankalin wanda ka sami dama daga cikinsu da muryarka ka kuma jawo su da rundunarka mahaya da na qasa; ka kuma yi tarayya da su cikin dukiyoyi da ‘ya’yaye; ka kuma yi musu alqawari.” Shaixan kuwa ba wani alqawari da yake yi musu sai na ruxi



السورة: Suratul Isra’i

الآية : 65

إِنَّ عِبَادِي لَيۡسَ لَكَ عَلَيۡهِمۡ سُلۡطَٰنٞۚ وَكَفَىٰ بِرَبِّكَ وَكِيلٗا

“Lalle bayina ba ka da iko a kansu.” Kuma Ubangijinka Ya isa zama Wakili



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 50

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ كَانَ مِنَ ٱلۡجِنِّ فَفَسَقَ عَنۡ أَمۡرِ رَبِّهِۦٓۗ أَفَتَتَّخِذُونَهُۥ وَذُرِّيَّتَهُۥٓ أَوۡلِيَآءَ مِن دُونِي وَهُمۡ لَكُمۡ عَدُوُّۢۚ بِئۡسَ لِلظَّـٰلِمِينَ بَدَلٗا

Kuma ka tuna lokacin da Muka ce da mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu”, sai suka yi sujjadar in ban da Iblis, ya kasance kuwa daga cikin aljannu, sai ya sava wa umarnin Ubangijinsa. Yanzu kwa riqe shi shi da zurriyarsa masoya ba Ni ba, alhali kuwa su maqiyanku ne? Wannan canji na azzalumai ya munana



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 116

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ أَبَىٰ

Kuma (ka tuna) lokacin da Muka ce da mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu” sai suka yi sujjadar sai Iblis ne kawai ya qi