فَقُلۡنَا يَـٰٓـَٔادَمُ إِنَّ هَٰذَا عَدُوّٞ لَّكَ وَلِزَوۡجِكَ فَلَا يُخۡرِجَنَّكُمَا مِنَ ٱلۡجَنَّةِ فَتَشۡقَىٰٓ
Sannan Muka ce: “Ya Adamu, lalle wannan maqiyinka ne kai da matarka, to kada (ku yarda) ya fitar da ku daga Aljanna, sai ka wahala
إِنَّ لَكَ أَلَّا تَجُوعَ فِيهَا وَلَا تَعۡرَىٰ
“Lalle (Allah) Ya yi maka alqawarin ba za ka ji yunwa ba a cikinta, kuma ba za ka yi tsiraici ba
وَأَنَّكَ لَا تَظۡمَؤُاْ فِيهَا وَلَا تَضۡحَىٰ
“Kuma lalle kai ba za ka ji qishi ba a cikinta, kuma ba za ka ji zafin rana ba.”
فَوَسۡوَسَ إِلَيۡهِ ٱلشَّيۡطَٰنُ قَالَ يَـٰٓـَٔادَمُ هَلۡ أَدُلُّكَ عَلَىٰ شَجَرَةِ ٱلۡخُلۡدِ وَمُلۡكٖ لَّا يَبۡلَىٰ
Sai Shaixan ya yi masa waswasi ya ce: “Ya Adamu, yanzu ba na nuna maka wata bishiya ta dawwama da kuma mulki wanda ba zai qare ba?”
وَلَقَدۡ صَدَّقَ عَلَيۡهِمۡ إِبۡلِيسُ ظَنَّهُۥ فَٱتَّبَعُوهُ إِلَّا فَرِيقٗا مِّنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Kuma haqiqa Iblisu ya tabbatar da zatonsa a kansu gaskiya ne[1], sai suka bi shi, in ban da wata qungiya ta muminai
1- Watau na cewa zai iya vatar da su ya raba su da gaskiya.
وَمَا كَانَ لَهُۥ عَلَيۡهِم مِّن سُلۡطَٰنٍ إِلَّا لِنَعۡلَمَ مَن يُؤۡمِنُ بِٱلۡأٓخِرَةِ مِمَّنۡ هُوَ مِنۡهَا فِي شَكّٖۗ وَرَبُّكَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٍ حَفِيظٞ
Shi kuwa ba shi da wani qarfi a kansu, sai dai (Mun yi haka ne) don Mu bayyana wanda yake imani da ranar lahira da kuma wanda yake cikin shakka game da ita. Ubangijinka kuwa Mai kiyaye komai ne
إِذۡ قَالَ رَبُّكَ لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ إِنِّي خَٰلِقُۢ بَشَرٗا مِّن طِينٖ
(Ka tuna) lokacin da Ubangijinka Ya ce da mala’iku: “Lalle Ni zan halicci wani mutum daga tavo
فَإِذَا سَوَّيۡتُهُۥ وَنَفَخۡتُ فِيهِ مِن رُّوحِي فَقَعُواْ لَهُۥ سَٰجِدِينَ
“To idan Na daidaita shi Na kuma busa masa ruhina, sai ku faxi kuna masu yi masa sujjada.”
فَسَجَدَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ كُلُّهُمۡ أَجۡمَعُونَ
Sai mala’iku dukkaninsu gaba xaya suka yi sujjada
إِلَّآ إِبۡلِيسَ ٱسۡتَكۡبَرَ وَكَانَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ
Sai Iblisa da ya yi girman kai ya kuma zama cikin kafirai
قَالَ يَـٰٓإِبۡلِيسُ مَا مَنَعَكَ أَن تَسۡجُدَ لِمَا خَلَقۡتُ بِيَدَيَّۖ أَسۡتَكۡبَرۡتَ أَمۡ كُنتَ مِنَ ٱلۡعَالِينَ
(Allah) Ya ce: “Ya kai Iblisa, me ya hana ka yin sujjada ga abin da Na halitta da hannayena biyu? Ka yi girman kai ne, ko kuwa da man can ka kasance daga masu nuna isa?”
قَالَ أَنَا۠ خَيۡرٞ مِّنۡهُ خَلَقۡتَنِي مِن نَّارٖ وَخَلَقۡتَهُۥ مِن طِينٖ
Sai ya ce: “Ni ai na fi shi; (domin) Ka halicce ni ne daga wuta, (shi) kuma Ka halicce shi daga tavo.”
قَالَ فَٱخۡرُجۡ مِنۡهَا فَإِنَّكَ رَجِيمٞ
(Sai Allah) Ya ce (da shi): “To ka fice daga cikinta (wato Aljanna) saboda kai lalle korarre ne (daga rahama)
وَإِنَّ عَلَيۡكَ لَعۡنَتِيٓ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلدِّينِ
“Kuma lalle la’antata tabbas ta hau kanka har zuwa ranar alqiyama.”
قَالَ رَبِّ فَأَنظِرۡنِيٓ إِلَىٰ يَوۡمِ يُبۡعَثُونَ
(Sai Iblisa) ya ce: “Ya Ubangijina, Ka saurara min har zuwa ranar da za a tashe su.”
قَالَ فَإِنَّكَ مِنَ ٱلۡمُنظَرِينَ
(Sai Allah) Ya ce: “To lalle kana cikin waxanda za a saurara wa
إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡوَقۡتِ ٱلۡمَعۡلُومِ
“Har zuwa ranar lokaci sananne.”
قَالَ فَبِعِزَّتِكَ لَأُغۡوِيَنَّهُمۡ أَجۡمَعِينَ
Sai ya ce: “To na rantse da girmanka tabbas zan vatar da su baki xaya
إِلَّا عِبَادَكَ مِنۡهُمُ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
“Sai dai bayinka waxanda aka tsarkake daga cikinsu.”
قَالَ فَٱلۡحَقُّ وَٱلۡحَقَّ أَقُولُ
(Allah) Ya ce: “Gaskiya (daga gare Ni take), kuma gaskiyar kawai Nake faxa!
لَأَمۡلَأَنَّ جَهَنَّمَ مِنكَ وَمِمَّن تَبِعَكَ مِنۡهُمۡ أَجۡمَعِينَ
“Tabbas zan cika Jahannama da kai da kuma waxanda suka bi ka baki xaya.”
وَأَنَّهُۥ كَانَ يَقُولُ سَفِيهُنَا عَلَى ٱللَّهِ شَطَطٗا
“Kuma lalle yadda lamarin yake, wani wawa daga cikinmu ya kasance yana faxar mummunar qarya game da Allah