السورة: Suratu Sad

الآية : 59

هَٰذَا فَوۡجٞ مُّقۡتَحِمٞ مَّعَكُمۡ لَا مَرۡحَبَۢا بِهِمۡۚ إِنَّهُمۡ صَالُواْ ٱلنَّارِ

(Za a ce da su): “Wannan ma wani gungun ne (na mabiya) mai afkawa tare da ku;” (sai shugabannin su ce): “Ba ma yin maraba da su.” Lalle (su duka) wuta za su shiga



السورة: Suratu Sad

الآية : 60

قَالُواْ بَلۡ أَنتُمۡ لَا مَرۡحَبَۢا بِكُمۡۖ أَنتُمۡ قَدَّمۡتُمُوهُ لَنَاۖ فَبِئۡسَ ٱلۡقَرَارُ

(Mabiyan kuma sai) su ce: “A’a, ku dai ne ba ma maraba da ku; ku ne kuka kawo mana shi (wannan mummunan sakamako);” to wannan matabbata ta munana



السورة: Suratu Sad

الآية : 61

قَالُواْ رَبَّنَا مَن قَدَّمَ لَنَا هَٰذَا فَزِدۡهُ عَذَابٗا ضِعۡفٗا فِي ٱلنَّارِ

Sai suka ce: “Ya Ubangijinmu, duk wanda ya kawo mana wannan (sakamakon) to Ka qara masa ninkin azaba a cikin wuta.”



السورة: Suratu Sad

الآية : 62

وَقَالُواْ مَا لَنَا لَا نَرَىٰ رِجَالٗا كُنَّا نَعُدُّهُم مِّنَ ٱلۡأَشۡرَارِ

Suka kuma ce: “Me ya sa ne ba ma ganin wasu mazaje[1] da muka kasance muna lissafa su cikin ashararai?


1- Suna nufin muminai waxanda suka riqa yi wa izgili a duniya, suna musu kallon vatattu.


السورة: Suratu Sad

الآية : 63

أَتَّخَذۡنَٰهُمۡ سِخۡرِيًّا أَمۡ زَاغَتۡ عَنۡهُمُ ٱلۡأَبۡصَٰرُ

“Shin mun xauke su ne ababen yi wa ba’a (a duniya), ko kuwa idanuwanmu ne suka bauxe ba sa hango su?”



السورة: Suratu Sad

الآية : 64

إِنَّ ذَٰلِكَ لَحَقّٞ تَخَاصُمُ أَهۡلِ ٱلنَّارِ

“Shin mun xauke su ne ababen yi wa ba’a (a duniya), ko kuwa idanuwanmu ne suka bauxe ba sa hango su?”



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 6

وَكَذَٰلِكَ حَقَّتۡ كَلِمَتُ رَبِّكَ عَلَى ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَنَّهُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِ

Kamar haka ne kuma kalmar Ubangijinka (ta azaba) ta tabbata a kan waxanda suka kafirta cewa, lalle su ‘yan wuta ne



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 46

ٱلنَّارُ يُعۡرَضُونَ عَلَيۡهَا غُدُوّٗا وَعَشِيّٗاۚ وَيَوۡمَ تَقُومُ ٱلسَّاعَةُ أَدۡخِلُوٓاْ ءَالَ فِرۡعَوۡنَ أَشَدَّ ٱلۡعَذَابِ

(Ita ce) wuta da za a riqa bijirar da su a gare ta safe da yamma; Ranar tashin alqiyama kuma za a ce: “Ku shigar da mutanen Fir’auna mafi tsananin azaba



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 47

وَإِذۡ يَتَحَآجُّونَ فِي ٱلنَّارِ فَيَقُولُ ٱلضُّعَفَـٰٓؤُاْ لِلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُوٓاْ إِنَّا كُنَّا لَكُمۡ تَبَعٗا فَهَلۡ أَنتُم مُّغۡنُونَ عَنَّا نَصِيبٗا مِّنَ ٱلنَّارِ

(Ka tuna) kuma lokacin da suke ta yin jayayya a cikin wuta, sai raunanan su riqa ce wa waxanda suka yi girman kai: “Lalle mun kasance mabiyanku (a duniya), to shin za ku iya xauke mana wani kaso na (azabar) wuta?”



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 48

قَالَ ٱلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُوٓاْ إِنَّا كُلّٞ فِيهَآ إِنَّ ٱللَّهَ قَدۡ حَكَمَ بَيۡنَ ٱلۡعِبَادِ

Waxanda suka yi girman kai sai su ce: “Lalle mu duka a cikinta muke, lalle Allah Ya riga Ya yi hukunci tsakanin bayi.”



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 74

إِنَّ ٱلۡمُجۡرِمِينَ فِي عَذَابِ جَهَنَّمَ خَٰلِدُونَ

Lalle masu manyan laifuka suna cikin azabar (wutar) Jahannama suna masu dawwama



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 75

لَا يُفَتَّرُ عَنۡهُمۡ وَهُمۡ فِيهِ مُبۡلِسُونَ

Ba a yanke musu ita (azabar), su kuwa masu yanke qaunar (fita) ne daga cikinta



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 76

وَمَا ظَلَمۡنَٰهُمۡ وَلَٰكِن كَانُواْ هُمُ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Ba Mu kuwa zalunce su ba, sai dai su ne suka kasance azzalumai



السورة: Suratu Qaf 

الآية : 24

أَلۡقِيَا فِي جَهَنَّمَ كُلَّ كَفَّارٍ عَنِيدٖ

(Aka ce da mala’ikun): “Ku jefa duk wani kafiri mai taurin kai cikin Jahannama



السورة: Suratu Qaf 

الآية : 25

مَّنَّاعٖ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٖ مُّرِيبٍ

“Mai yawan hana alheri, mai ta’addanci, mai shakka



السورة: Suratu Qaf 

الآية : 26

ٱلَّذِي جَعَلَ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ فَأَلۡقِيَاهُ فِي ٱلۡعَذَابِ ٱلشَّدِيدِ

“Wanda ya sanya wani abin bauta daban tare da Allah, saboda haka ku jefa shi cikin azaba mai tsanani.”



السورة: Suratul Qamar

الآية : 47

إِنَّ ٱلۡمُجۡرِمِينَ فِي ضَلَٰلٖ وَسُعُرٖ

Lalle masu manyan laifuka suna cikin vata da azabar wuta



السورة: Suratul Qamar

الآية : 48

يَوۡمَ يُسۡحَبُونَ فِي ٱلنَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمۡ ذُوقُواْ مَسَّ سَقَرَ

Ranar da za a ja su cikin wuta a kan fuskokinsu (a ce da su): “Ku xanxani azabar wutar Saqara.”



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 41

وَأَصۡحَٰبُ ٱلشِّمَالِ مَآ أَصۡحَٰبُ ٱلشِّمَالِ

Ma’abota hannun hagu kuma, mamakin qasqancin ma’abota hannun hagu!



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 42

فِي سَمُومٖ وَحَمِيمٖ

Suna cikin iska mai tsananin zafi da kuma tafasasshen ruwa



السورة: Suratul Jinn

الآية : 15

وَأَمَّا ٱلۡقَٰسِطُونَ فَكَانُواْ لِجَهَنَّمَ حَطَبٗا

“Amma kuma karkatattu, to sun kasance makamashi ne ga (wutar) Jahannama.”



السورة: Suratul Jinn

الآية : 23

إِلَّا بَلَٰغٗا مِّنَ ٱللَّهِ وَرِسَٰلَٰتِهِۦۚ وَمَن يَعۡصِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ فَإِنَّ لَهُۥ نَارَ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدًا

“Sai dai isar da aike daga Allah da kuma saqwanninsa. Duk kuwa waxanda suka sava wa Allah da Manzonsa, to lalle suna da wutar Jahannama, suna madawwama a cikinta har abada.”



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 37

فَأَمَّا مَن طَغَىٰ

To (a wannan ranar) duk wanda ya yi xagawa



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 38

وَءَاثَرَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا

Ya kuma fifita rayuwar duniya



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 39

فَإِنَّ ٱلۡجَحِيمَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle (wutar) Jahimu ita ce makoma



السورة: Suratul Buruj

الآية : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُواْ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ ثُمَّ لَمۡ يَتُوبُواْ فَلَهُمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمۡ عَذَابُ ٱلۡحَرِيقِ

Lalle waxanda suka azabtar da muminai maza da muminai mata sannan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, suna kuma da azabar quna



السورة: Suratul Bayyina

الآية : 6

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ فِي نَارِ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَآۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمۡ شَرُّ ٱلۡبَرِيَّةِ

Lalle waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushirikai suna cikin wutar Jahannama suna madawwama a cikinta. Waxannan su ne mafiya sharrin halitta



السورة: Suratul Qari’a

الآية : 8

وَأَمَّا مَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ

Amma kuma duk wanda ma’aunan ayyukansa suka yi shafal



السورة: Suratul Qari’a

الآية : 9

فَأُمُّهُۥ هَاوِيَةٞ

To shi makomarsa (wutar) Hawiya ce



السورة: Suratul Qari’a

الآية : 10

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا هِيَهۡ

Kuma me ya sanar da kai mece ce ita?