هَٰذَا فَوۡجٞ مُّقۡتَحِمٞ مَّعَكُمۡ لَا مَرۡحَبَۢا بِهِمۡۚ إِنَّهُمۡ صَالُواْ ٱلنَّارِ
(Za a ce da su): “Wannan ma wani gungun ne (na mabiya) mai afkawa tare da ku;” (sai shugabannin su ce): “Ba ma yin maraba da su.” Lalle (su duka) wuta za su shiga
قَالُواْ بَلۡ أَنتُمۡ لَا مَرۡحَبَۢا بِكُمۡۖ أَنتُمۡ قَدَّمۡتُمُوهُ لَنَاۖ فَبِئۡسَ ٱلۡقَرَارُ
(Mabiyan kuma sai) su ce: “A’a, ku dai ne ba ma maraba da ku; ku ne kuka kawo mana shi (wannan mummunan sakamako);” to wannan matabbata ta munana
قَالُواْ رَبَّنَا مَن قَدَّمَ لَنَا هَٰذَا فَزِدۡهُ عَذَابٗا ضِعۡفٗا فِي ٱلنَّارِ
Sai suka ce: “Ya Ubangijinmu, duk wanda ya kawo mana wannan (sakamakon) to Ka qara masa ninkin azaba a cikin wuta.”
وَقَالُواْ مَا لَنَا لَا نَرَىٰ رِجَالٗا كُنَّا نَعُدُّهُم مِّنَ ٱلۡأَشۡرَارِ
Suka kuma ce: “Me ya sa ne ba ma ganin wasu mazaje[1] da muka kasance muna lissafa su cikin ashararai?
1- Suna nufin muminai waxanda suka riqa yi wa izgili a duniya, suna musu kallon vatattu.
أَتَّخَذۡنَٰهُمۡ سِخۡرِيًّا أَمۡ زَاغَتۡ عَنۡهُمُ ٱلۡأَبۡصَٰرُ
“Shin mun xauke su ne ababen yi wa ba’a (a duniya), ko kuwa idanuwanmu ne suka bauxe ba sa hango su?”
إِنَّ ذَٰلِكَ لَحَقّٞ تَخَاصُمُ أَهۡلِ ٱلنَّارِ
“Shin mun xauke su ne ababen yi wa ba’a (a duniya), ko kuwa idanuwanmu ne suka bauxe ba sa hango su?”
وَكَذَٰلِكَ حَقَّتۡ كَلِمَتُ رَبِّكَ عَلَى ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَنَّهُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِ
Kamar haka ne kuma kalmar Ubangijinka (ta azaba) ta tabbata a kan waxanda suka kafirta cewa, lalle su ‘yan wuta ne
ٱلنَّارُ يُعۡرَضُونَ عَلَيۡهَا غُدُوّٗا وَعَشِيّٗاۚ وَيَوۡمَ تَقُومُ ٱلسَّاعَةُ أَدۡخِلُوٓاْ ءَالَ فِرۡعَوۡنَ أَشَدَّ ٱلۡعَذَابِ
(Ita ce) wuta da za a riqa bijirar da su a gare ta safe da yamma; Ranar tashin alqiyama kuma za a ce: “Ku shigar da mutanen Fir’auna mafi tsananin azaba
وَإِذۡ يَتَحَآجُّونَ فِي ٱلنَّارِ فَيَقُولُ ٱلضُّعَفَـٰٓؤُاْ لِلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُوٓاْ إِنَّا كُنَّا لَكُمۡ تَبَعٗا فَهَلۡ أَنتُم مُّغۡنُونَ عَنَّا نَصِيبٗا مِّنَ ٱلنَّارِ
(Ka tuna) kuma lokacin da suke ta yin jayayya a cikin wuta, sai raunanan su riqa ce wa waxanda suka yi girman kai: “Lalle mun kasance mabiyanku (a duniya), to shin za ku iya xauke mana wani kaso na (azabar) wuta?”
قَالَ ٱلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُوٓاْ إِنَّا كُلّٞ فِيهَآ إِنَّ ٱللَّهَ قَدۡ حَكَمَ بَيۡنَ ٱلۡعِبَادِ
Waxanda suka yi girman kai sai su ce: “Lalle mu duka a cikinta muke, lalle Allah Ya riga Ya yi hukunci tsakanin bayi.”
إِنَّ ٱلۡمُجۡرِمِينَ فِي عَذَابِ جَهَنَّمَ خَٰلِدُونَ
Lalle masu manyan laifuka suna cikin azabar (wutar) Jahannama suna masu dawwama
لَا يُفَتَّرُ عَنۡهُمۡ وَهُمۡ فِيهِ مُبۡلِسُونَ
Ba a yanke musu ita (azabar), su kuwa masu yanke qaunar (fita) ne daga cikinta
وَمَا ظَلَمۡنَٰهُمۡ وَلَٰكِن كَانُواْ هُمُ ٱلظَّـٰلِمِينَ
Ba Mu kuwa zalunce su ba, sai dai su ne suka kasance azzalumai
أَلۡقِيَا فِي جَهَنَّمَ كُلَّ كَفَّارٍ عَنِيدٖ
(Aka ce da mala’ikun): “Ku jefa duk wani kafiri mai taurin kai cikin Jahannama
مَّنَّاعٖ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٖ مُّرِيبٍ
“Mai yawan hana alheri, mai ta’addanci, mai shakka
ٱلَّذِي جَعَلَ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ فَأَلۡقِيَاهُ فِي ٱلۡعَذَابِ ٱلشَّدِيدِ
“Wanda ya sanya wani abin bauta daban tare da Allah, saboda haka ku jefa shi cikin azaba mai tsanani.”
إِنَّ ٱلۡمُجۡرِمِينَ فِي ضَلَٰلٖ وَسُعُرٖ
Lalle masu manyan laifuka suna cikin vata da azabar wuta
يَوۡمَ يُسۡحَبُونَ فِي ٱلنَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمۡ ذُوقُواْ مَسَّ سَقَرَ
Ranar da za a ja su cikin wuta a kan fuskokinsu (a ce da su): “Ku xanxani azabar wutar Saqara.”
وَأَصۡحَٰبُ ٱلشِّمَالِ مَآ أَصۡحَٰبُ ٱلشِّمَالِ
Ma’abota hannun hagu kuma, mamakin qasqancin ma’abota hannun hagu!
فِي سَمُومٖ وَحَمِيمٖ
Suna cikin iska mai tsananin zafi da kuma tafasasshen ruwa
وَأَمَّا ٱلۡقَٰسِطُونَ فَكَانُواْ لِجَهَنَّمَ حَطَبٗا
“Amma kuma karkatattu, to sun kasance makamashi ne ga (wutar) Jahannama.”
إِلَّا بَلَٰغٗا مِّنَ ٱللَّهِ وَرِسَٰلَٰتِهِۦۚ وَمَن يَعۡصِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ فَإِنَّ لَهُۥ نَارَ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدًا
“Sai dai isar da aike daga Allah da kuma saqwanninsa. Duk kuwa waxanda suka sava wa Allah da Manzonsa, to lalle suna da wutar Jahannama, suna madawwama a cikinta har abada.”
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ
To (a wannan ranar) duk wanda ya yi xagawa
وَءَاثَرَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا
Ya kuma fifita rayuwar duniya
فَإِنَّ ٱلۡجَحِيمَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ
To lalle (wutar) Jahimu ita ce makoma
إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُواْ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ ثُمَّ لَمۡ يَتُوبُواْ فَلَهُمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمۡ عَذَابُ ٱلۡحَرِيقِ
Lalle waxanda suka azabtar da muminai maza da muminai mata sannan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, suna kuma da azabar quna
إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ فِي نَارِ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَآۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمۡ شَرُّ ٱلۡبَرِيَّةِ
Lalle waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushirikai suna cikin wutar Jahannama suna madawwama a cikinta. Waxannan su ne mafiya sharrin halitta
وَأَمَّا مَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ
Amma kuma duk wanda ma’aunan ayyukansa suka yi shafal
فَأُمُّهُۥ هَاوِيَةٞ
To shi makomarsa (wutar) Hawiya ce
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا هِيَهۡ
Kuma me ya sanar da kai mece ce ita?