السورة: Suratu Qaf 

الآية : 30

يَوۡمَ نَقُولُ لِجَهَنَّمَ هَلِ ٱمۡتَلَأۡتِ وَتَقُولُ هَلۡ مِن مَّزِيدٖ

A ranar da za Mu ce da Jahannama: “Shin kin cika?” (Ita) kuma ta ce: “Shin akwai wani qari?”



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 42

فِي سَمُومٖ وَحَمِيمٖ

Suna cikin iska mai tsananin zafi da kuma tafasasshen ruwa



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 43

وَظِلّٖ مِّن يَحۡمُومٖ

Da kuma inuwa ta turnuqun hayaqi



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 44

لَّا بَارِدٖ وَلَا كَرِيمٍ

Ba mai sanyi ba, kuma ba mai daraja ba



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 51

ثُمَّ إِنَّكُمۡ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلۡمُكَذِّبُونَ

“Sannan lalle ku kuma waxannan vatattu masu qaryatawa



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 52

لَأٓكِلُونَ مِن شَجَرٖ مِّن زَقُّومٖ

“Tabbas za ku ci daga bishiyar Zaqqumu[1]


1- Watau wata bishiya ce mafi muni da sharri a wutar jahannama.


السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 53

فَمَالِـُٔونَ مِنۡهَا ٱلۡبُطُونَ

“Sannan za ku cika cikunanku da ita



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 54

فَشَٰرِبُونَ عَلَيۡهِ مِنَ ٱلۡحَمِيمِ

“Sannan za ku sha tafasasshen ruwa a kanta



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 55

فَشَٰرِبُونَ شُرۡبَ ٱلۡهِيمِ

“Sannan za ku sha irin shan raquma masu jin qishirwa.”



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 56

هَٰذَا نُزُلُهُمۡ يَوۡمَ ٱلدِّينِ

Wannan ita ce gararsu a ranar sakamako



السورة: Suratut Tahrim

الآية : 6

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ قُوٓاْ أَنفُسَكُمۡ وَأَهۡلِيكُمۡ نَارٗا وَقُودُهَا ٱلنَّاسُ وَٱلۡحِجَارَةُ عَلَيۡهَا مَلَـٰٓئِكَةٌ غِلَاظٞ شِدَادٞ لَّا يَعۡصُونَ ٱللَّهَ مَآ أَمَرَهُمۡ وَيَفۡعَلُونَ مَا يُؤۡمَرُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku kare kawunanku da iyalanku daga wuta (wadda) makamashinta mutane ne da duwatsu, masu kula da ita mala’iku ne masu kaushin hali, masu tsananin gaske, ba sa sava wa Allah abin da Ya umarce su, suna kuma aikata abin da ake umartar su



السورة: Suratul Mulk

الآية : 6

وَلِلَّذِينَ كَفَرُواْ بِرَبِّهِمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Waxanda kuma suka kafirce wa Ubangijinsu suna da azabar Jahannama; makoma kuwa ta munana



السورة: Suratul Mulk

الآية : 7

إِذَآ أُلۡقُواْ فِيهَا سَمِعُواْ لَهَا شَهِيقٗا وَهِيَ تَفُورُ

Idan aka jefa su a cikinta sai su ji kururuwarta, tana tafarfasa



السورة: Suratul Mulk

الآية : 8

تَكَادُ تَمَيَّزُ مِنَ ٱلۡغَيۡظِۖ كُلَّمَآ أُلۡقِيَ فِيهَا فَوۡجٞ سَأَلَهُمۡ خَزَنَتُهَآ أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ نَذِيرٞ

Tana kusa da ta kekkece saboda tsananin fushi; duk sanda aka jefa wata tawaga a cikinta sai masu tsaron ta su tambaye su: “Shin mai gargaxi bai zo muku ba?”



السورة: Suratul Haqqa

الآية : 31

ثُمَّ ٱلۡجَحِيمَ صَلُّوهُ

Sannan ku shigar da shi (wutar) Jahimu



السورة: Suratul Haqqa

الآية : 32

ثُمَّ فِي سِلۡسِلَةٖ ذَرۡعُهَا سَبۡعُونَ ذِرَاعٗا فَٱسۡلُكُوهُ

Sannan ku sa shi cikin sarqa mai tsawo kamu saba’in



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 15

كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Faufau! Lalle ita (wutar) Laza ce



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 16

نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ

Mai xaxxaye fatar kai



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 17

تَدۡعُواْ مَنۡ أَدۡبَرَ وَتَوَلَّىٰ

Tana kiran wanda ya juya ya ba da baya



السورة: Suratul Ma’arij

الآية : 18

وَجَمَعَ فَأَوۡعَىٰٓ

Ya kuma tara (dukiya) sai ya voye (ta)



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 26

سَأُصۡلِيهِ سَقَرَ

(Allah ya ce): Da sannu zan shigar da shi (wutar) Saqara



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 27

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سَقَرُ

Me ya sanar da kai abin da ake ce wa Saqara?



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 28

لَا تُبۡقِي وَلَا تَذَرُ

Ba ta ragewa kuma ba ta barin (komai)



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 29

لَوَّاحَةٞ لِّلۡبَشَرِ

Mai xaxxaye fata ce



السورة: Suratul Insan

الآية : 4

إِنَّآ أَعۡتَدۡنَا لِلۡكَٰفِرِينَ سَلَٰسِلَاْ وَأَغۡلَٰلٗا وَسَعِيرًا

Lalle Mun tanadar wa kafirai sarqoqi da ququmai da wutar Sa’ira



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 30

ٱنطَلِقُوٓاْ إِلَىٰ ظِلّٖ ذِي ثَلَٰثِ شُعَبٖ

Ku tafi zuwa wata inuwa mai rassa uku



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 31

لَّا ظَلِيلٖ وَلَا يُغۡنِي مِنَ ٱللَّهَبِ

Ba mai ba da inuwa ba kuma ba mai karewa daga harshen wuta ba



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 32

إِنَّهَا تَرۡمِي بِشَرَرٖ كَٱلۡقَصۡرِ

Haqiqa ita tana jefa tartsatsi kamar qaton gini



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 33

كَأَنَّهُۥ جِمَٰلَتٞ صُفۡرٞ

Kai ka ce su raquma ne baqaqe



السورة: Suratun Naba’i

الآية : 21

إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتۡ مِرۡصَادٗا

Lalle Jahannama ta kasance madakata ce